< 1 Chronicles 9 >
1 Therfor al Israel was noumbrid, and the summe of hem was writun in the book of kyngis of Israel and of Juda; and thei weren translatid in to Babiloyne for her synne.
Haka aka lissafta dukan Isra’ila a tarihin zuriyoyi a littafin sarakunan Isra’ila. Aka kwasa mutanen Yahuda zuwa zaman bauta a Babilon domin rashin aminci.
2 Sotheli thei that dwelliden first in her citees, and in the possessiouns of Israel, and the preestis, and the dekenes, and Natyneys, dwelliden in Jerusalem.
To, na farkon da aka sāke zaunar da su a mallakarsu a garuruwansu, su ne waɗansu Isra’ilawa, firistoci, Lawiyawa da kuma masu hidimar haikali.
3 Of the sones of Juda, and of the sones of Beniamyn, also of the sones of Effraym, and of Manasses;
Waɗanda suke daga Yahuda, daga Benyamin, da kuma daga Efraim da Manasse waɗanda suka zauna a Urushalima su ne,
4 Othi, the sone of Amyud, sone of Semry, sone of Omroy, sone of Bonny, of the sones of Phares, the sone of Juda;
Uttai ɗan Ammihud, ɗan Omri, ɗan Imri, ɗan Bani, zuriyar Ferez ɗan Yahuda.
5 and of Sylom, Asia, the firste gendrid, and his sones;
Na mutanen Shilo kuwa su ne, Asahiya ɗan fari da’ya’yansa maza.
6 sotheli of the sones of Zaray, Heuel, and hise britheren; sixe hundrid fourescore and ten.
Na mutanen Zera su ne, Yewuyel. Mutane daga Yahuda sun kai 690.
7 Forsothe of the sones of Beniamyn; Salo, the sone of Mosollam, the sones of Odoia, the sones of Asana,
Na Benyamin su ne, Sallu ɗan Meshullam, ɗan Hodawiya, ɗan Hassenuwa;
8 and Jobanya, the sone of Jerobam, and Ela, the sone of Ozi, the sones of Mochozi, and Mosollam, the sone of Saphacie, sone of Rahuel, sone of Jebanye, and the britheren of hem,
Ibnehiya ɗan Yeroham; Ela ɗan Uzzi, ɗan Mikri; da Meshullam ɗan Shefatiya, ɗan Reyuwel, ɗan Ibniya.
9 bi her meynees; nyne hundrid sixe and fifti. Alle these weren princes of her kynredis by the housis of her fadris.
Mutane daga Benyamin, kamar yadda aka lissafta zuriyarsu, sun kai 956. Dukan waɗannan mutane kawunan iyalansu ne.
10 Forsothe of the preestis, Joiada, Jozarib, and Jachym;
Na firistoci su ne, Yedahiya; Yehoyarib; Yakin;
11 and Azarie, the sone of Helchie, sone of Mosollam, sone of Sadoch, sone of Maraioth, sone of Achitob, was bischop of the hows of the Lord.
Azariya ɗan Hilkiya, ɗan Meshullam, ɗan Zadok, ɗan Merahiyot, ɗan Ahitub, shugaban da yake lura da gidan Allah;
12 Forsothe Adaias, sone of Jeroam, sone of Phasor, sone of Melchia, and Masaia, sone of Adihel, sone of Jezra, sone of Mosollam, sone of Mosselamoth, sone of Emyner,
Adahiya ɗan Yeroham, ɗan Fashhur, ɗan Malkiya; da Ma’asai ɗan Adiyel, ɗan Yazera, ɗan Meshullam, ɗan Meshillemit, ɗan Immer.
13 also her britheren, prynces bi her meynees, weren a thousynde seuene hundrid and fourescoore, men strongeste in bodili myyt, to make the werk of seruyce in the hows of the Lord.
Firistocin da suke kawunan iyalai, sun kai 1,760. Dukansu ƙwararru ne, masu hakkin hidima a cikin gidan Allah.
14 Forsothe of dekenes, Semeya, the sone of Assub, sone of Ezricam, sone of Asebyn, of the sones of Merary;
Na Lawiyawa su ne, Shemahiya ɗan Hasshub, ɗan Azrikam, ɗan Hashabiya, mutumin Merari;
15 also Balthasar the carpenter, and Galebeth, and Machama, sone of Mycha, sone of Zechri, sone of Asaph,
Bakbakkar, Heresh, Galal da Mattaniya ɗan Mika, ɗan Zikri, ɗan Asaf;
16 and Obdias, sone of Semey, sone of Calaal, sone of Idithum, and Barachie, the sone of Asa, sone of Helcana, that dwellide in the porchis of Methophati.
Obadiya ɗan Shemahiya, ɗan Galal, ɗan Yedutun; da Berekiya ɗan Asa, ɗan Elkana, wanda ya zauna a ƙauyukan Netofawa.
17 Sotheli the porteris weren Sellum, and Achub, and Thelmon, and Achyman, and the britheren of hem; Sellum was the prince;
Matsaran ƙofofi su ne, Shallum, Akkub, Talmon, Ahiman da’yan’uwansu. Shallum ne babbansu
18 til to that tyme thei kepten bi her whilis in the yate of the kyng at the eest, of the sones of Leuy.
da aka ajiye a Ƙofar Sarki a gabas, har zuwa wannan lokaci. Waɗannan su ne matsaran ƙofofi na sansanin Lawiyawa.
19 Sellum forsothe, the sone of Chore, sone of Abiasaph, sone of Chore, with hise britheren, and with the hows of his fadir; these ben the sones of Chore on the werkis of the seruyce, keperis of the porchis of the tabernacle, and the meynees of hem kepten bi whilis the entryng of the castelis of the Lord.
Shallum ɗan Kore, ɗan Ebiyasaf, ɗan Kora, da’yan’uwansa matsaran ƙofofi daga iyalin (mutanen Kohat) su suke da hakkin tsaron madogaran ƙofar Tenti kamar dai yadda kakanninsu suka kasance da hakkin tsaron mashigin mazaunin Ubangiji.
20 Forsothe Phynees, the sone of Eleazar, was the duyk of hem bifor the Lord.
A dā Finehas ɗan Eleyazar ne yake lura da matsaran, kuma Ubangiji ya kasance tare da shi.
21 Sotheli Zacarie, the sone of Mosollam, was porter of the yate of the tabernacle of witnessyng.
Zakariya ɗan Meshelemiya shi ne mai tsaro a mashigin Tentin Sujada.
22 Alle these chosun in to porteris bi yatis weren twei hundrid and twelue, and weren discryued in her owne townes, which dekenes Dauid and Samuel, the prophete, ordeyneden in her feith,
Duka-duka, waɗanda aka zaɓa don su zama matsaran madogaran ƙofa sun kai 212. Aka rubuta su zuriya-zuriya a ƙauyukansu. Dawuda da Sama’ila mai duba ne suka sa matsaran a wurarensu na aminci.
23 both hem and the sones of hem in the doris of the hows of the Lord, and in the tabernacle of witnessyng, bi her whiles.
Su da zuriyarsu, su suke lura da tsaron ƙofofin gidan Ubangiji, gidan da ake kira Tenti.
24 Porteris weren bi foure coostis, that is, at the eest, and at the west, and at the north, and at the south.
Matsaran suna a kusurwoyi huɗu, gabas, yamma, arewa da kudu.
25 Forsothe her britheren dwelliden in townes, and camen in her sabatis fro tyme til to tyme.
’Yan’uwansu a ƙauyukansu sukan zo lokaci, lokaci su yi ayyukansu kwana bakwai, bakwai.
26 Al the noumbre of porteris was bitakun to these foure dekenes, and thei kepten the chaumbris, and the tresours of the hows of the Lord.
Amma manyan matsara huɗu, waɗanda suke Lawiyawa, an danƙa musu hakkin lura da ɗakuna da kuma wuraren ajiya a gidan Allah.
27 Also thei dwelliden in her kepyngis bi the cumpas of the temple of the Lord, that whanne tyme were, thei schulden opene the yatis eerli.
Sukan kwana a kewayen gidan Allah, domin dole su tsare shi; kuma su suke lura da mabuɗi don buɗewa a kowace safiya.
28 Men of her kyn weren also on the vessels of seruyce; for the vessels weren borun in at noumbre, and weren borun out of hem.
Waɗansunsu su ne suke lura da kayayyakin da ake amfani da su a hidimar haikali; sukan ƙirga su sa’ad da ake shigar da su da sa’ad da ake fitar da su.
29 And thei that hadden the vesselis of seyntuarie bitakun to her kepyng, weren souereyns on flour, and wyn, and oile, and encense, and swete smellinge spyceries.
An sa waɗansu su lura da kayayyakin da kuma dukan waɗansu kayan wuri mai tsarki, da kuma gari da ruwan inabi, da mai, turare da kuma kayan yaji.
30 Sotheli the sones of preestis maden oynementis of swete smellynge spiceries.
Amma waɗansu firistoci ne suke harhaɗa kayan yajin.
31 And Mathatias dekene, the firste gendrid sone of Sellum of the kynrede of Chore, was the souereyn of alle thingis that weren fried in the friyng panne.
Wani Balawe mai suna Mattitiya, ɗan farin Shallum mutumin Kora ne aka danƙa masa hakkin toya burodin miƙawa.
32 Sotheli men of the sones of Caath, the britheren of hem, weren on the looues of settyng forth, that thei schulden make redi euere newe looues bi ech sabat.
Waɗansu’yan’uwansu Kohatawa ne suke lura da shiryawa burodin da ake kaiwa a tebur a kowane Asabbaci.
33 These ben the princis of chauntouris bi the meynees of Leuytis, that dwelliden in chaumbris, so that thei schulden serue contynueli dai and nyyt in her seruyce.
Waɗanda suke mawaƙa, kawunan iyalan Lawiyawa, sukan zauna a ɗakunan haikali kuma ba sa yin waɗansu ayyuka domin su suke da hakkin aiki dare da rana.
34 The heedis of Leuitis bi her meynees, the princes, dwelliden in Jerusalem.
Dukan waɗannan su ne kawunan iyalan Lawiyawa, manya kamar yadda aka lissafta su a zuriyarsu, kuma suna zama a Urushalima.
35 Forsothe there dwelliden in Gabaon; Jaiel, the fadir of Gabaon, and the name of his wijf Maacha;
Yehiyel mahaifin Gibeyon ya zauna a Gibeyon. Matarsa ita ce Ma’aka
36 Abdon, his firste gendrid sone, and Sur, and Cys, and Baal,
ɗansa na fari kuwa shi ne Abdon, sai Zur, Kish, Ba’al, Ner, Nadab,
37 and Ner, and Nadab, and Gedor, and Ahaio, and Zacharie, and Macelloth; forsothe Macelloth gendride Semmaa;
Gedor, Ahiyo, Zakariya da Miklot.
38 these dwelliden euene ayens her britheren in Jerusalem, with her britheren.
Miklot shi ne mahaifin Shimeyam. Su ma sun zauna kusa da danginsu a Urushalima.
39 Sotheli Ner gendride Cys, and Cys gendride Saul, and Saul gendride Jonathan, and Melchisue, and Abynadab, and Hisbaal.
Ner shi mahaifin Kish, Kish mahaifin Shawulu, kuma Shawulu shi ne mahaifin Yonatan, Malki-Shuwa, Abinadab da Esh-Ba’al.
40 Forsothe the sone of Jonathan was Myribaal, and Myribaal gendride Mycha.
Ɗan Yonatan shi ne, Merib-Ba’al wanda shi ne mahaifin Mika.
41 Sotheli the sones of Micha weren Phiton, and Malech, and Thara;
’Ya’yan Mika maza su ne, Fiton, Melek, Tareya da Ahaz.
42 forsothe Aaz gendride Jara, and Jara gendride Alamath, and Azmoth, and Zamri; and Zamri gendride Moosa,
Ahaz shi ne mahaifin Yada, Yada shi ne mahaifin Alemet, Azmawet da Zimri, Zimri kuwa shi ne mahaifin Moza.
43 sotheli Moosa gendride Baana, whose sone Raphaia gendride Elisa, of whom Esel was gendrid.
Moza shi ne mahaifin Bineya; Refahiya, Eleyasa da kuma Azel.
44 Forsothe Esel hadde sixe sones bi these names, Ezricam, Bochru, Hismael, Saria, Obdia, Anan; these weren the sones of Hesel.
Azel yana da’ya’ya maza shida, kuma ga sunayensu. Azrikam, Bokeru, Ishmayel, Sheyariya, Obadiya da Hanan. Waɗannan su ne’ya’yan Azel maza.