< 1 Chronicles 23 >

1 Therfor Dauid was eld and ful of daies, and ordeynede Salomon, his sone, kyng on Israel.
Sa’ad da Dawuda ya tsufa yana kuma da cikakken shekaru, ya sa ɗansa Solomon sarki bisa Isra’ila.
2 And he gaderide togidere alle the princes of Israel, and the preestis, and dekenes;
Ya kuma tattara dukan shugabannin Isra’ila a wuri ɗaya, haka kuma ya yi da firistoci da Lawiyawa.
3 and the dekenes weren noumbrid fro twenti yeer and aboue, and eiyte and thretti thousynde of men weren foundun.
Aka ƙidaya Lawiyawan da suke’yan shekaru talatin da haihuwa ko fiye, suka kai wajen mutum dubu talatin da takwas.
4 And foure and twenty thousynde men weren chosun of hem, and weren departid in to the seruyce of the hows of the Lord; sotheli of souereyns, and iugis, sixe thousynde;
Dawuda ya ce, “Cikin waɗannan, dubu ashirin da huɗu za su lura da aikin haikalin Ubangiji, dubu shida su zama manyan na ma’aikata da alƙalai.
5 forsothe foure thousynde `porteris weren, and so many syngeris, syngynge to the Lord in orguns, whiche Dauid hadde maad for to synge.
Dubu huɗu su zama matsaran ƙofofi, dubu huɗu kuma su yabi Ubangiji da kayayyakin bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe waɗanda na tanada saboda wannan manufa.”
6 And Dauid departide hem bi the whilis of the sones of Leuy, that is, of Gerson, and of Caath, and Merary.
Dawuda ya rarraba Lawiyawa ƙungiya-ƙungiya bisa ga’ya’yan Lawi maza. Gershon, Kohat da Merari.
7 And the sones of Gerson weren Leedan and Semeye.
Na Gershonawa, Ladan da Shimeyi.
8 The sones of Leedan weren thre, the prince Jehiel, and Ethan, and Johel.
’Ya’yan Ladan maza su ne, Yehiyel na farko, Zetam da Yowel, su uku ne duka.
9 The sones of Semei weren thre, Salamyth, and Oziel, and Aram; these weren the princes of the meynees of Leedan.
’Ya’yan Shimeyi maza su ne, Shelomot, Haziyel da Haran, su uku ne duka. Waɗannan su ne kawunan iyalan Ladan.
10 Forsothe the sones of Semeye weren Leeth, and Ziza, and Yaus, and Baria, these foure weren the sones of Semei.
’Ya’yan Shimeyi maza kuwa su ne, Yahat, Zina, Yewush da Beriya. Waɗannan su ne’ya’yan Shimeyi maza, su huɗu ne duka.
11 Sotheli Leeth was the formere, and Ziza the secounde; forsothe Yaus and Baria hadden not ful many sones, and therfor thei weren rikenyd in o meynee and oon hows.
Yahat shi ne na fari, Ziza kuma na biyu, amma Yewush da Beriya ba su haifi’ya’ya maza da yawa ba; saboda haka aka ƙidaya su kamar iyali ɗaya a wurin rabon aiki.
12 The sones of Caath weren foure, Amram, and Ysaac, Ebron, and Oziel.
’Ya’yan Kohat maza su ne, Amram, Izhar, Hebron da Uzziyel, su huɗu ne duka.
13 The sones of Amram weren Aaron and Moyses; and Aaron was departid, that he schulde mynystre in the hooli thing of hooli thingis, he and hise sones with outen ende, and to brenne encense to the Lord bi his custom, and to blesse his name with outen ende.
’Ya’yan Amram maza su ne, Haruna da Musa. Haruna shi ne aka keɓe, shi da zuriyarsa har abada, don su tsarkake kayayyakin mafi tsarki, su miƙa hadayu a gaban Ubangiji, su yi hidima a gabansa su kuma furta albarku a cikin sunansa har abada.
14 Also the sones of Moyses, man of God, weren noumbrid in the lynage of Leuy.
An ƙidaya aka kuma haɗa’ya’yan Musa maza mutumin Allah a sashen kabilar Lawi.
15 The sones of Moises weren Gerson and Elieser.
’Ya’yan Musa maza su ne, Gershom da Eliyezer.
16 The sones of Gerson; `Subuhel the firste.
Zuriyar Gershom su ne, Shebuwel ne ɗan fari.
17 Sotheli the sones of Eliezer weren Roboya the firste, and othere sones weren not to Eliezer; forsothe the sones of Roboia weren multipliede ful miche.
Zuriyar Eliyezer su ne, Rehabiya ne ɗan fari. Eliyezer ba shi da waɗansu’ya’ya maza, amma’ya’yan Rehabiya maza sun yi yawa.
18 The sones of Isaar; `Salumuth the firste.
’Ya’yan Izhar maza su ne, Shelomit ne ɗan fari.
19 The sones of Ebron; `Jerian the firste, Amarias the secounde, Jaziel the thridde, Jethamaan the fourthe.
’Ya’yan Hebron maza su ne, Yeriya na fari, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da Yekameyam na huɗu.
20 The sones of Oziel; `Mycha the firste, Jesia the secounde.
’Ya’yan Uzziyel maza su ne, Mika na fari da Isshiya na biyu.
21 The sones of Merari weren Mooli and Musi. The sones of Mooli weren Eleazar, and Cys.
’Ya’yan Merari maza su ne, Mali da Mushi.’Ya’yan Mali maza su ne, Eleyazar da Kish.
22 Sotheli Eleazar was deed, and hadde not sones, but douytris; and the sones of Cys, the britheren of hem, weddiden hem.
Eleyazar ya mutu ba’ya’yan maza, yana da’ya’ya mata ne kawai.’Yan’uwansu,’ya’yan Kish maza, suka aure su.
23 The sones of Musi weren thre, Mooli, and Heder, and Jerymuth.
’Ya’yan Mushi maza su ne, Mali, Eder da Yeremot, su uku ne duka.
24 These weren the sones of Leuy in her kynredis and meynees, prynces bi whilis, and noumbre of alle heedis, that diden the trauel of the seruyce of the hows of the Lord, fro twenti yeer and aboue.
Waɗannan ne zuriyar Lawi bisa ga iyalansu, kawunan iyalai kamar yadda aka rubuta su a ƙarƙashin sunayensu aka kuma ƙirga kowa, wato, masu aikin da suke’yan shekara ashirin da haihuwa ko fiye waɗanda suka yi hidima a cikin haikalin Ubangiji.
25 For Dauid seide, The Lord God of Israel hath youe reste to his puple, and a dwellyng in Jerusalem til in to with outen ende;
Gama Dawuda ya ce, “Tun da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya ba da hutu ga mutanensa, ya kuma zo ya zauna a Urushalima har abada,
26 and it schal not be the office of dekenes for to bere more the tabernacle, and alle vessels therof for to mynystre.
Lawiyawa ba sa ƙara bukata su ɗauki tabanakul ko kuwa waɗansu kayayyakin da ake amfani da su a hidima.”
27 Also bi the laste comaundementis of Dauid the noumbre of the sones of Leuy schulen be rikened fro twenti yeer and aboue;
Bisa ga umarnin ƙarshe na Dawuda, za a ƙidaya Lawiyawa daga’yan shekara ashirin ko fiye.
28 and thei schulen be vndir the hond of the sones of Aaron in to the worschipe of the hows of the Lord, in porchis, and in chaumbris, and in the place of clensyng, and in the seyntuarie, and in alle werkis of the seruyce of the temple of the Lord.
Aikin Lawiyawa shi ne su taimaki zuriyar Haruna a hidimar haikalin Ubangiji; su lura da filaye da kuma ɗakunan da suke gefe, su tsarkake dukan kayayyaki masu tsarki, su kuma yi waɗansu ayyuka a gidan Allah.
29 Forsothe preestis schulen be ouer the looues of proposicioun, and to the sacrifice of flour, and to the pastis sodun in watir, and to the therf looues, and friyng panne, and to hoot flour, and to seenge, and ouer al weiyte and mesure.
Su ne za su lura da burodin da aka ajiye a tebur, lallausan gari don hadaya ta gari, waina marar yisti, toyawa da kwaɓawa, da kuma dukan awon yawa da kuma girman abubuwa.
30 Forsothe the dekenes schulen be, that thei stonde eerli, for to knowleche and synge to the Lord, and lijk maner at euentide,
Su ne kuma za su tsaya kowace safiya su yi godiya, su kuma yabi Ubangiji. Za su kuma yi haka da yamma
31 as wel in the offryng of brent sacrifices of the Lord, as in sabatis, and kalendis, and othere solempnytees, bi the noumbre and cerymonyes of eche thing contynueli bifor the Lord;
da kuma a duk sa’ad da aka miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a Asabbatai da bukukkuwan Sabon Wata da kuma a ƙayyadaddun bukukkuwa, za su yi hidima a gaban Ubangiji kullum bisa ga yawan da aka tsara da kuma a hanyar da aka tsara musu.
32 and that thei kepe the obseruaunces of the tabernacle of the boond of pees of the Lord, and the custum of the seyntuarie, and the obseruaunce of the sones of Aaron, her britheren, that thei mynystre in the hows of the Lord.
A haka kuwa Lawiyawa suka yi ayyukansu don Tentin Sujada, don Wuri Mai Tsarki da kuma a ƙarƙashin’yan’uwansu zuriyar Haruna, saboda hidimar haikalin Ubangiji.

< 1 Chronicles 23 >