< 1 Chronicles 17 >
1 Forsothe whanne Dauid dwellide in his hows, he seide to Nathan, the prophete, Lo! Y dwelle in an hows of cedris; sotheli the arke of boond of pees of the Lord is vndur skynnys.
Bayan Dawuda ya zauna a fadansa, sai ya ce wa annabi Natan, “Ga ni, ina zama a fadar da aka yi da al’ul, yayinda akwatin alkawarin Ubangiji yana a ƙarƙashin tenti.”
2 And Nathan seide to Dauid, Do thou alle thingis that ben in thin herte, for God is with thee.
Natan ya amsa wa Dawuda ya ce, “Duk abin da kake tunani a zuciya, ka yi, gama Allah yana tare da kai.”
3 Therfor in that nyyt the word of the Lord was maad to Nathan,
A daren nan maganar Allah ta zo wa Natan cewa,
4 and seide, Go thou, and speke to Dauid, my seruaunt, The Lord seith these thingis, Thou schalt not bilde to me an hows to dwelle in;
“Ka tafi ka faɗa wa bawana Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ba kai ba ne za ka gida mini gidan da zan zauna a ciki.
5 for Y `dwellide not in an hows, fro that tyme in which Y ledde Israel out of the lond of Egipt til to this dai, but euere Y chaungide places of tabernacle, and dwellide in a tente with al Israel.
Ban taɓa zama a gida daga ranar da na fito da Isra’ila daga Masar ba har wa yau. Na yi ta yawo daga gefen da aka kafa tenti zuwa wani, daga wannan wuri zuwa wancan.
6 Where I spak nameli to oon of the iugis of Israel, to which I comaundide that thei schulde fede my puple, and seide, Whi `bildidist thou not to me an hous of cedre?
Duk inda na tafi tare da Isra’ilawa, na taɓa ce wa wani daga cikin shugabanninsu waɗanda na umarta su yi kiwon mutanena, “Don me ba ku gida mini gidan al’ul ba?”’
7 Now therfor thou schalt speke thus to my seruaunt Dauid, The Lord of oostis seith these thingis, Y took thee, whanne thou suedist the floc in the lesewis, that thou schuldist be duyk on my puple Israel;
“Yanzu, ka faɗa wa bawana Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, na ɗauke ka daga makiyaya da kuma daga bin garke, don ka zama mai mulki a bisa mutanena Isra’ila.
8 and Y was with thee whidur euere thou yedist, and Y killide alle thin enemyes bifor thee, and Y made to thee an name as of oon of the grete men that ben maad worschipful, ether `famouse, in erthe.
Na kasance tare da kai ko’ina ka tafi, na kuma yanke dukan abokan gābanka a gabanka. Yanzu zan sa sunanka kamar sunayen mutane mafi girma na duniya.
9 And Y yaf a place to my puple Israel; it schal be plauntid, and schal dwelle there ynne, and it schal no more be moued, and the sones of wickydnesse schulen not defoule hem,
Zan kuma tanada wuri domin mutanena Isra’ila, zan kuma kafa su saboda za su kasance da gidan kansu ba kuwa za a ƙara damunsu ba. Mugayen mutane ba za su ƙara zaluntar su ba, yadda suka yi da farko
10 as fro the bigynnyng, fro the daies in whiche Y yaf iugis to my puple Israel; and Y made lowe alle thin enemyes. Therfor Y telle to thee, that the Lord schal bilde an hows to thee.
da kuma suka yi tun lokacin da na sa shugabanni a bisa mutanen Isra’ila. Zan rinjaye dukan abokan gābanka. “‘Na furta maka cewa Ubangiji zai gina maka gida,
11 And whanne thou hast fillid thi daies, that thou go to thi fadris, Y schal reise thi seed after thee, that schal be of thi sones, and Y schal stablische his rewme;
sa’ad da kwanakinka suka ƙare ka kuma tafi don ka kasance da kakanninka, zan tā da ɗaya cikin’ya’yanka maza, daga zuriyarka yă gāje ka, zan kuma kafa mulkinka.
12 he schal bilde to me an hows, and Y schal make stidefast his seete til in to with outen ende.
Shi ne zai gina gida domina, zan kuma kafa sarautarsa har abada.
13 Y schal be to hym in to a fadir, and he schal be to me in to a sone; and Y schal not do my mersi fro hym, as Y took awei fro hym that was bifore thee;
Zan zama Ubansa, zai kuma zama ɗana. Ba zan taɓa ɗauke ƙaunata daga gare shi, kamar yadda na ɗauke ta daga wanda ya riga ka ba.
14 and Y schal ordeyne hym in myn hows and in my rewme til in to with outen ende; and his trone schal be moost stidefast with outen ende.
Zan sa shi a bisa gidana da mulkina har abada; kujerar sarautarsa za tă kahu har abada.’”
15 Bi alle these wordis, and bi al this reuelacioun, so Nathan spak to Dauid.
Natan ya faɗa wa Dawuda dukan kalmomin wahayin nan.
16 And whanne kyng Dauid hadde come, and hadde sete bifore the Lord, he seide, Lord God, who am Y, and what is myn hows, that thou schuldist yyue siche thingis to me?
Sai Sarki Dawuda ya shiga ya zauna a gaban Ubangiji ya ce, “Wane ne ni, ya Ubangiji Allah, kuma wane ne iyalina, da ka kawo ni har zuwa nan?
17 But also this is seyn litil in thi siyt, and therfor thou spakest on the hows of thi seruaunt, yhe, in to tyme to comynge; and hast maad me worthi to be biholdun ouer alle men.
Kuma sai ka ce wannan bai isa ba a idonka, ya Allah, ka yi magana game da nan gaba na gidan bawanka. Ka dube ni sai ka ce ni ne mafi ɗaukaka cikin mutane, ya Ubangiji Allah.
18 My Lord God, what may Dauid adde more, sithen thou hast so glorified thi seruaunt, and hast knowe hym?
“Me kuma Dawuda zai ce maka saboda girmamawar da ka yi wa bawanka? Gama ka san bawanka,
19 Lord, for thi seruaunt thou hast do bi thin herte al this grete doyng, and woldist that alle grete thingis be knowun.
Ya Ubangiji. Gama saboda bawanka da kuma bisa ga nufinka, ka yi wannan babban abu, ka kuma sanar da dukan manyan alkawura.
20 Lord, noon is lijk thee, and noon other God is with oute thee, of alle whiche we herden with oure eeris.
“Babu wani kamar ka, ya Ubangiji, babu kuma Allah sai kai, kamar yadda muka ji da kunnuwanmu.
21 For who is anothir as thi puple Israel, o folc in erthe, to whom God yede, to delyuere and make a puple to hym silf, and to caste out bi his greetnesse and dredis naciouns fro the face therof, which he delyuerede fro Egipt?
Wane ne kuma yake kamar mutanenka Isra’ila, al’umma guda a duniya wadda Allahnta ya fita don yă fanshi mutane wa kansa, ya kuma yi suna wa kansa, ya kuma aikata manyan abubuwa masu banmamaki masu banrazana ta wurin korin al’ummai daga gaban mutanenka, waɗanda ka fansa daga Masar?
22 And thou hast set thi puple Israel in to a puple to thee til in to with outen ende, and thou, Lord, art maad the God therof.
Ka mai da mutanenka Isra’ila na kanka har abada, kuma kai, ya Ubangiji, ka zama Allahnsu.
23 Now therfor, Lord, the word which thou hast spoke to thi seruaunt, and on his hows, be confermed with outen ende, and do, as thou spake;
“Yanzu kuwa, Ubangiji, bari alkawarin da ka yi game da bawanka da gidansa yă kahu har abada. Yi kamar yadda ka yi alkawari,
24 and thi name dwelle, and be magnefied `with outen ende; and be it seid, The Lord of oostis is God of Israel, and the hous of Dauid, his seruaunt, dwellynge bifor hym.
saboda zai kahu kuma sunanka zai zama mai girma har abada. Sa’an nan mutane za su ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki, Allah a bisa Isra’ila, Allahn Isra’ila ne!’ Kuma gidan bawanka Dawuda zai kahu a gabanka.
25 For thou, my Lord God, hast maad reuelacioun to the eere of thi seruaunt, that thou woldist bilde to hym an hous; and therfor thi seruaunt foond trist, that he preie bifor thee.
“Kai, Allahna, ka bayyana ga bawanka cewa za ka gina gida dominsa. Ta haka bawanka ya sami ƙarfin gwiwa ya yi addu’a gare ka.
26 Now therfor, Lord, thou art God, and hast spoke to thi seruaunt so grete benefices;
Ya Ubangiji, kai ne Allah! Ka yi alkawari abubuwa masu kyau wa bawanka.
27 and thou hast bigunne to blesse the hous of thi seruaunt, that it be euer bifore thee; for, Lord, for thou blessist, it schal be blessid with outen ende.
Yanzu ka ji daɗi don ka albarkace gidan bawanka, don yă ci gaba har abada a gabanka; gama kai, ya Ubangiji, ka albarkace shi, ya kuma sami albarka ke nan har abada.”