< 1 Chronicles 15 >
1 And he made to hym housis in the citee of Dauid, and he bildide `a place to the arke of the Lord, and araiede a tabernacle to it.
Bayan Dawuda ya yi gine-gine wa kansa a Birnin Dawuda, sai ya shirya wuri domin akwatin alkawarin Allah, ya kuma kafa tenti dominsa.
2 Thanne Dauid seide, It is vnleueful, that the arke of God be borun of `ony thing no but of the dekenes, whiche the Lord chees to bere it, and `for to mynystre to hym `til in to with outen ende.
Sa’an nan Dawuda ya ce, “Babu wani sai ko Lawiyawa kaɗai za su ɗauka akwatin alkawarin Allah, gama Ubangiji ya zaɓe su su ɗauka akwatin alkawarin Ubangiji su kuma yi hidima a gabansa har abada.”
3 And he gaderide togidere al Israel in to Jerusalem, that the arke of God schulde be brouyt in to `his place, which he hadde maad redy to it;
Dawuda ya tattara dukan Isra’ila a Urushalima don su haura da akwatin alkawarin Ubangiji zuwa wurin da aka shirya dominsa.
4 also and he gaderide togidere the sones of Aaron, and the dekenes;
Ya tattara zuriyar Haruna a wuri ɗaya da kuma Lawiyawa.
5 of the sones of Caath Vriel was prince, and hise britheren two hundrid and twenti;
Daga zuriyar Kohat, Uriyel shugaba da dangi 120;
6 of the sones of Merari Asaya was prince, and hise britheren two hundrid and thritti;
daga zuriyar Merari Asahiya shugaba da dangi 220;
7 of the sones of Gerson the prince was Johel, and hise britheren an hundrid and thretti;
daga zuriyar Gershom, Yowel shugaba da dangi 130;
8 of the sones of Elisaphan Semei was prynce, and hise britheren two hundrid;
daga zuriyar Elizafan, Shemahiya shugaba da dangi 200;
9 of the sones of Ebroun Heliel was prince, and hise britheren foure score;
daga zuriyar Hebron, Eliyel shugaba da dangi 80;
10 of the sones of Oziel Amynadab was prince, and hise britheren an hundrid and twelue.
daga zuriyar Uzziyel, Amminadab shugaba da dangi 112.
11 And Dauid clepide Sadoch and Abiathar preestis, and the dekenes Vriel, Asaie, Johel, Semeie, Eliel, and Amynadab; and seide to hem,
Sa’an nan Dawuda ya kira Zadok da Abiyatar, firistoci, tare da Uriyel, Asahiya, Yowel, Shemahiya, Eliyel da Amminadab, Lawiyawa.
12 Ye that ben princes of the meynees of Leuy, be halewid with youre britheren, and brynge ye the arke of the Lord God of Israel to the place, which is maad redi to it;
Ya ce musu, “Ku ne kawunan iyalan Lawiyawa; ku da’yan’uwanku Lawiyawa, sai ku tsarkake kanku ku hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila, zuwa wurin da na shirya dominsa.
13 lest, as at the bigynnyng, for ye weren not present, the Lord smoot vs, and now it be don, if we don ony vnleueful thing.
Domin ku, Lawiyawa ba ku haura da shi da farko ba ne ya sa Ubangiji Allahnmu ya husata a kanmu. Ba mu tambaye shi game da yadda za mu yi shi a hanyar da aka ƙayyade ba.”
14 Therfor the preestis and dekenes weren halewid, that thei schulden bere the arke of the Lord God of Israel.
Saboda haka firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu don su hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
15 And the sones of Leuy token the arke of God with barris on her schuldris, as Moises comaundide bi the word of the Lord.
Sai Lawiyawa suka ɗauki akwatin alkawarin Allah da sanduna a kafaɗunsu, kamar yadda Musa ya umarta bisa ga maganar Ubangiji.
16 And Dauid seide to the princes of dekenes, that thei schulden ordeyne of her britheren syngeris in orguns of musikis, that is, in giternes, and harpis, and symbalis; that the sown of gladnesse schulde sowne an hiy.
Dawuda ya faɗa wa shugabannin Lawiyawa su sa’yan’uwansu su zama mawaƙa don su rera waƙoƙi masu farin ciki, da kayayyakin bushe-bushe, da kaɗe-kaɗe, molaye, garayu da ganguna.
17 And thei ordeyneden dekenes, Heman, the sone of Johel, and of hise britheren, Asaph, the sone of Barachie; sotheli of the sones of Merary, britheren of hem, thei ordeyneden Ethan,
Saboda haka Lawiyawa suka zaɓi Heman ɗan Yowel, da Asaf ɗan Berekiya daga cikin’yan’uwansu. Daga iyalin Merari kuma aka zaɓi Etan ɗan Kushahiya.
18 the sone of Casaye, and the britheren of hem with hem; in the secunde ordre `thei ordeyneden Zacarie, and Ben, and Jazihel, and Semyramoth, and Jahiel, `and Am, Heliab, and Benaye, and Maasie, and Mathathie, and Eliphalu, and Mathenye, and Obededon, and Jehiel, porteris;
Tare da su kuma’yan’uwansa da suke biye bisa ga matsayi. Wato, Zakariya, Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ben, Ma’asehiya, Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom da Yehiyel, matsaran ƙofofi.
19 forsothe `thei ordeyneden the syngeris Eman, Asaph, and Ethan, sownynge in brasun cymbalis;
Mawaƙan nan Heman, Asaf da Etan, ne za su buga kugen tagulla.
20 sotheli Zacarie, and Oziel, and Semyramoth, and Jahihel, and Ham, and Eliab, and Maasie, and Banaie, sungun pryuetees in giternes; forsothe Mathathie,
Zakariya, Aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ma’asehiya da Benahiya, ne za su kaɗa molaye masu murya sama-sama, bisa ga alamot.
21 and Eliphalu, and Mathenye, and Obededom, and Jehiel, and Ozazym, sungen in harpis for the eiytithe, and epynychion, `that is, victorie `be to God ouercomere;
Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom, Yehiyel da Azaziya, ne za su ja garayu masu murya ƙasa-ƙasa bisa ga sheminit.
22 forsothe Chinonye, the prince of dekenes, and of profecie, was souereyn to biforsynge melodie, for he was ful wijs;
Kenaniya, shugaban Lawiyawa, shi ne mai bi da waƙoƙi. Wannan hakkinsa ne, gama shi gwani ne a wannan fanni.
23 and Barachie, and Elchana, weren porters of the arke; forsothe Sebenye,
Berekiya da Elkana, ne za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
24 and Josaphath, and Mathanael, and Amasaye, and Zacarie, and Banaye, and Eliezer, preestis, sowneden with trumpis bifor the arke of the Lord; and Obededom, and Achymaas, weren porteris of the arke.
Shebaniya, Yoshafat, Netanel, Amasai, Zakariya, Benahiya da Eliyezer firistoci, su ne za su busa ƙahoni a gaban akwatin alkawarin Allah. Obed-Edom da Yehiya su ma za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
25 Therfor Dauid, and the grettere men in birthe of Israel, and the tribunes, yeden to brynge the arke of boond of pees of the Lord fro the hows of Obededom with gladnesse.
Sai Dawuda da dattawan Isra’ila da shugabannin ƙungiyoyi dubu suka haura don su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga gidan Obed-Edom, da farin ciki.
26 And whanne God hadde helpid the dekenes that baren the arke of boond of pees of the Lord, seuene bolis and seuene rammes weren offrid.
Domin Allah ya taimaki Lawiyawan da suke ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, aka miƙa hadayar bijimai bakwai da raguna bakwai.
27 Forsothe Dauid was clothid with a white stole, and alle the dekenes that baren the arke, and the syngeris, and Chononye, the prince of profecie among syngeris, weren clothid in white stolis; forsothe also Dauid was clothid with a lynun surplijs.
To, fa, Dawuda yana saye da kyakkyawar rigar lilin, kamar yadda dukan Lawiyawa waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawarin suka sa, da kuma yadda mawaƙa, da Kenaniya, wanda yake bi da waƙar mawaƙan ya sa. Dawuda kuma ya sa efod lilin.
28 And al Israel ledden forth the arke of boond of pees of the Lord, and sowneden in ioiful song, and in sown of clariouns, and in trumpis, and cymbalis, and giternis, and harpis.
Sai dukan Isra’ila suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji da sowa, da ƙarar ƙahonin raguna da busan ƙahoni, da na ganguna, suna kuma kaɗa molaye da garayu.
29 And whanne the arke of boond of pees of the Lord hadde come to the citee of Dauid, Mychol, the douytir of Saul, bihelde forth bi a wyndowe, and sche siy king Dauyd daunsynge and pleiynge; and sche dispiside hym in hir herte.
Yayinda akwatin alkawarin Ubangiji yake shiga Birnin Dawuda, Mikal’yar Shawulu ta leƙa daga taga. Sa’ad da ta ga Sarki Dawuda yana rawa yana shagali, sai ta rena masa wayo a zuciyarta.