< 1 Chronicles 11 >
1 Therfor al Israel was gaderid to Dauid in Ebron, and seide, We ben thi boon and thi fleisch;
Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
2 also yisterdai and the thridde dai ago, whanne Saul regnede yit on Israel, thou it were that leddist out and leddist in Israel; for `thi Lord God seide to thee, Thou schalt fede my puple Israel, and thou schalt be prince on it.
A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
3 Therfor alle the gretter in birthe of Israel camen to the kyng in Ebron; and Dauid maad with hem a boond of pees bifor the Lord, and thei anoyntiden hym kyng on Israel, bi the word of the Lord, which he spak in the hond of Samuel.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
4 Therfor Dauid yede, and al Israel, in to Jerusalem; this Jerusalem is Jebus, where Jebuseis enhabiteris of the lond weren.
Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
5 And thei that dwelliden at Jebus seiden to Dauid, Thou schalt not entre hidur. Forsothe Dauid took the hiy tour of Syon, which is the citee of Dauid;
suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
6 and he seide, Ech man that `sleeth first Jebusei, schal be prince and duyk. Therfor Joab, sone of Saruye, stiede first, and was maad prince.
Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
7 Sotheli Dauid dwellide in the hiy tour, and therfor it was clepid the cytee of Dauid;
Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
8 and he bildide the citee in cumpas fro Mello til to the cumpas; forsothe Joab bildide the tother part of the citee.
Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
9 And Dauid profitide goynge and wexynge, and the Lord of oostis was with hym.
Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
10 These ben the princes of the stronge men of Dauid, that helpiden hym, that he schulde be kyng on al Israel, bi the word of the Lord which he spak to Israel.
Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
11 And this is the noumbre of the stronge men of Dauid; Jesbaam, the sone of Achamony, was prince among thretti; this reiside his schaft ethir spere on thre hundrid woundid men in o tyme.
Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
12 And after hym was Eleazar, the sone of his fadris brothir, and was `a man of Ahoit, which Eleazar was among thre miyti men.
Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
13 This was with Dauid in Aphesdomyn, whanne Filisteis weren gaderid to o place in to batel; and a feeld of that cuntrey was ful of barli, and the puple fledde fro the face of Filisteis.
Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
14 This Eleazar stood in the myddis of the feeld, and defendide it; and whanne he hadde slayn Filisteis, the Lord yaf greet helthe to his puple.
Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
15 Sotheli thre of thritti princes yeden doun to the stoon, wher ynne Dauid was, to the denne of Odolla, whanne Filisteis settiden tentis in the valey of Raphaym.
Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
16 Forsothe Dauid was in a strong hold, and the stacioun, `that is, the oost gaderid, of Filisteis was in Bethleem.
A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
17 Therfor Dauid desiride watir, and seide, Y wolde, that sum man yaf to me water of the cisterne of Bethleem, which is in the yate.
Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
18 Therfor these thre yeden thoruy the myddil of the castelis of Filisteis, and drowen watir of the cisterne of Bethleem, that was in the yate, and thei brouyten to Dauid, that he schulde drynke; and Dauid nolde `drynke it, but rather he offride it to the Lord, and seide, Fer be it,
Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
19 that Y do this thing in the siyt of my God, and that Y drynke the blood of these men, for in the perel of her lyues thei brouyten watir to me; and for this cause he nolde drynke. Thre strongeste men diden these thingis.
Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
20 Also Abisai, the brother of Joab, he was the prince of thre men, and he reiside his schaft ayens thre hundrid woundid men; and he was moost named among thre,
Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
21 among the secounde thre he was noble, and the prince of hem; netheles he cam not til to the firste thre.
Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
22 Banaye, the sone of Joiada, strongest man of Capsael, that dide many werkis; he killide two stronge men of Moab; and he yede doun, and killide a lioun in the myddil of a cisterne, in the tyme of snow;
Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
23 and he killide a man of Egipt, whos stature was of fyue cubitis, and he hadde a spere as the beem of webbis; therfor Banaye yede doun to hym with a yerde, and rauyschide the spere, which he held in the hond, and killide hym with his owne spere.
Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
24 Banaye, the sone of Joiada, dide these thingis, that was moost named among thre stronge men, and was the firste among thretti;
Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
25 netheles he cam not til to the thre; sotheli Dauid settide hym at his eere.
Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
26 Forsothe the strongeste men `in the oost weren Asael, the brother of Joab, and Eleanan, the sone of his fadris brothir of Bethleem,
Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
27 Semynoth Arorites, Helles Phallonytes, Iras,
Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
28 the sone of Acces of Thecue, Abieser of Anathot,
Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
29 Sobochay Sochites, Ylai Achoytes,
Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
30 Maray Nethophatithes, Heles, the sone of Banaa, Nethophatithes, Ethaa,
Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
31 the sone of Rabai, of Gabaath of the sones of Beniamyn; Banaye Pharatonythes, men of the stronde Gaas,
Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
32 Abihel Arabatithes, Azmoth Baruanythes, Eliaba Salaonythes,
Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
33 the sones of Assem Gesonythes, Jonathan, the sone of Saga, Ararithes, Achiam,
Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
34 the sone of Achar, Ararites,
’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
35 Eliphal, the sone of Mapher,
Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
36 Mechoratithes, Ahya Phellonythes,
Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
37 Asrahi Carmelites, Neoray,
Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
38 the sone of Thasbi, Johel, the brother of Nathan, Mabar, the sone of Aggaray, Selech Ammonythes,
Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
39 Nooray Berothites, the squyer of Joab, sone of Saruye,
Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
40 Iras Jetreus, Gareb Jethreus,
Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
42 the sone of Ooli, Adyna, the sone of Segar Rubenytes, prince of Rubenytis, and thritti men with hym;
Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
43 Hanan, the sone of Macha, and Josaphath Mathanythes, Ozias Astarothites,
Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
44 Semma and Jahel, the sones of Hotayn Aroerites,
Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
45 Ledihel, the sone of Zamri, and Joha, his brother, Thosaythes,
Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
46 Hehiel Maanytes, Jerybay and Josia, the sones of Helnaen, Jethma Moabites,
Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
47 Heliel, and Obed, and Jasihel of Masobia.
Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.