< Revelation 14 >
1 Then I looked and behold a Lamb standing on mount Sion, and with Him an hundred forty and four thousand, having his Father's name written on their foreheads.
Sai na duba na ga Dan Ragon yana tsaye a kan Dutsen Sihiyona. Tare da shi akwai mutum dubu dari da arba'in da hudu wadanda aka rubuta sunansa da sunan Ubansa a goshinsu.
2 And I heard a voice from heaven, like the noise of many waters, and as the sound of great thunder; and I heard the sound of harpers playing on their harps:
Na ji wata murya daga sama mai kara kamar kogin ruwa mai gudu da kuma aradu mai kara. Muryar da na ji ta yi kama da masu molo suna kada molonsu.
3 and they sung as it were a new song before the throne; and before the four living ones, and the elders: and none could learn the song, but the hundred and forty four thousand, who are redeemed from the earth.
Suka raira sabuwar waka a gaban kursiyin da kuma gaban rayayyun halittun nan hudu, da kuma dattawan. Ba mai iya koyon wakar nan sai dai mutum 144, 000 nan wadanda aka fanso daga duniya.
4 These are they who were not defiled with women; for they are virgins: these are they who follow the Lamb whithersoever He goeth: these were redeemed from among men, as the first-fruits unto God and the Lamb.
Wadannan sune wadanda basu kazantar da kansu da mata ba, gama sun kebe kansu da tsarki daga halin jima'i. Wadannan ne ke bin Dan Ragon duk inda ya tafi. Aka fanso su daga cikin mutane domin su zama nunan fari domin Allah da Dan Ragon.
5 And in their mouth was found no guile: for they are blameless before the throne of God.
Ba a iske karya a bakinsu ba; ba su da aibi.
6 And I saw another angel flying in the midst of heaven, having the everlasting gospel, to preach to those that dwell upon the earth, to every nation, and tribe, and tongue, (aiōnios )
Na ga wani mala'ika na firiya a tsakiyar sararin sama, wanda yake da madawwamin sako na labari mai dadi domin a sanar da ita ga mazaunan duniya - ga kowacce al'umma, da kabila, da harshe, da kuma jama'a. (aiōnios )
7 and people, saying with a loud voice, Fear God, and give glory to Him; for the time of his judgement is come: and worship Him that made the heaven, and the earth, and the sea, and the fountains of waters.
Yayi kira da babbar murya, “Ku ji tsoron Allah, ku daukaka shi. Gama sa'arsa ta hukunci ta yi. Yi masa sujada, shi wanda ya yi sama da kasa, da teku, da kuma mabulbular ruwa.”
8 And another angel followed, saying, Babylon the great city is fallen, is fallen; because she made all nations drink of the wine of her furious fornication.
Sai wani malai'ka, malaika na biyu, ya biyo yana cewa, “Ta fadi, Babila mai girma ta fadi, wadda ta rinjayi dukan al'ummai su sha ruwan inabin fasikancinta.”
9 And a third angel followed them, saying with a loud voice, If any one worship the beast and his image, and receive the mark on his forehead,
Wani mala'ika - na uku - ya biyo su da murya mai karfi yana cewa, “Duk wanda ya yi sujada ga dabban da kuma siffarsa, ya karbi alama a goshinsa ko a hannunsa,
10 or on his hand, he also shall drink of the wine of God's indignation poured forth without mixture, in the cup of his wrath; and shall be tormented with fire and brimstone, in the presence of the holy angels, and in the presence of the Lamb.
shi ma zai sha daga ruwan inabin fushin Allah, ruwan inabi da aka zuba tsantsa cikin kokon fushinsa. Wanda ya sha shi za a azabtar da shi da wuta, da farar wuta, a gaban tsarkakan mala'ikun Allah da kuma Dan Ragon.
11 And the smoke of their torment ascendeth for ever and ever: and they have no rest, day and night, who worship the beast and his image, and whosoever receiveth the mark of his name. (aiōn )
Hayaki daga azabarsu yana tashi sama har abada abadin, kuma ba su da hutu dare ko rana - wadannan masu sujada ga dabban da siffarsa da kuma dukan wadanda suka karbi alamar sunansa. (aiōn )
12 Here is the patience of the saints: here are they that keep the commandments of God, and the faith of Jesus.
Wannan shine kira domin hakurin jimrewa na wadanda ke da tsarki, wadanda suke biyayya ga dokokin Allah da bangaskiya cikin Yesu.”
13 And I heard a voice from heaven, saying unto me, Write, Blessed are the dead, that die in the Lord, from henceforth: yea, saith the Spirit, for they rest from their labors and their works do follow them.
Na ji murya daga sama cewa, “Rubuta wannan: Masu albarka ne matattu da suka mutu cikin Ubangiji.” Ruhu yace, 'I' domin sun huta daga wahalarsu, gama ayyukansu na biye da su.”
14 And I saw, and behold, a white cloud, and one sitting on the cloud like the Son of man; having on his head a golden crown, and in his hand a sharp sickle.
Na duba sai ga farin gajimare. Zaune a kan gajimaren akwai wani kamar Dan Mutum. Yana da kambin zinariya a kansa da lauje mai kaifi a hannunsa.
15 And another angel came out of the temple, crying with a loud voice to Him that sat upon the cloud, Put in thy sickle and reap; for the time to reap is come, for the harvest of the earth is ripe.
Sai wani malaika ya fito daga haikalin, ya yi kira da murya mai karfi ga wanda ke zaune kan gajimare: “Dauki laujenka ka fara girbi, domin lokacin girbin duniya ya yi.”
16 And He that sat upon the cloud put forth his sickle on the earth, and the earth was reaped.
Sai wanda ke zaune a kan gajimaren ya wurga laujensa bisa kan duniya, aka kuma girbe duniya.
17 And another angel came out of the temple which is in heaven, and he also had a sharp sickle.
Wani mala'ika ya fito daga haikali a sama, shi ma yana da kakkaifan lauje.
18 And another angel came out from the altar, who had power over the fire; and he called out with a loud cry to Him that had the sharp sickle, saying, Put in thy sharp sickle, and gather the clusters of the vine of the earth, for its grapes are ripe.
Sai wani mala'ika ya fito daga bagadin kona turare, wanda yake da iko kan wutar. Ya yi kira da murya mai karfi ga wanda yake rike da kakkaifan lauje, “Ka dauki kakkaifan laujenka ka tattara nonnan innabi daga itacen inabin na duniya, gama inabin ya nuna.”
19 And the angel put forth his sickle to the earth, and stript the vine of the earth, and cast the grapes into the great wine-press of God's wrath.
Mala'ikan ya jefa laujensa duniya ya tattara girbin inabin duniya. Ya zuba shi a cikin babbar taskar wurin matsar ruwan inabi na fushin Allah.
20 And the wine-press was trodden without the city, and blood came out of the wine-press, even to the horses bridles, a thousand six hundred furlongs off.
Aka tattake wurin matsar inabin a bayan birni, jini ya yi ta gudu daga wurin matsar inabin, ya kai kamar tsawon linzami a bakin doki, har mil dari biyu.