< Matthew 24 >

1 And as Jesus went out, and was departing from the temple, his disciples came to observe to Him the magnificent buildings.
Yesu ya bar haikali ke nan, yana cikin tafiya sai almajiransa suka zo wurinsa don su ja hankalinsa ga gine-ginen haikali.
2 But Jesus said unto them, Do ye see all these things? Verily I tell you, there shall not be left here one stone upon another, that shall not be demolished.
Sai Yesu ya ce, “Kun ga duk waɗannan abubuwa? Gaskiya nake gaya muku, ba wani dutse a nan da za a bari a kan wani; duk za a rushe.”
3 And when He was got to the mount of olives, the disciples came to Him in private and said, Tell us when these things shall be, and what shall be the sign of thy coming, and of the end of the world. (aiōn g165)
Da Yesu yana zaune a Dutsen Zaitun, almajiran suka zo wurinsa a ɓoye. Suka ce, “Gaya mana, yaushe ne wannan zai faru, mece ce alamar zuwanka da kuma ta ƙarshen zamani?” (aiōn g165)
4 And Jesus answered them, See that no one deceive you:
Yesu ya amsa, “Ku lura fa, kada wani yă ruɗe ku.
5 for many shall come in my name saying, I am the Christ, and shall deceive many.
Gama mutane da yawa za su zo cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne Kiristi,’ za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
6 And ye shall hear of wars and rumors of wars, but be not troubled; for all these must indeed come to pass, but the end is not yet.
Za ku ji labarin yaƙe-yaƙe da kuma jita-jitarsu, sai dai ku lura kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru, amma ƙarshen tukuna.
7 For nation shall rise against nation, and kingdom against kingdom; and there shall be famines, and pestilences, and earthquakes in several places:
Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki yă tasar wa mulki. Za a yi yunwa da girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam.
8 all which are but the beginning of sorrows.
Dukan waɗannan fa, mafarin azabar naƙudar haihuwa ne.
9 Then shall they afflict you, and kill you; and ye shall be hated by all nations for my name:
“Sa’an nan za a bashe ku don a tsananta muku a kuma kashe ku, dukan al’ummai za su ƙi ku saboda ni.
10 and then will many take offense, and betray one another, and hate one another: and many false prophets will rise up and deceive many:
A wannan lokaci, da yawa za su juya daga bangaskiya, su ci amana su kuma ƙi juna,
11 and because iniquity shall abound,
annabawan ƙarya da yawa za su firfito su kuma ruɗi mutane da yawa.
12 the love of many will grow cold.
Saboda ƙaruwar mugunta, ƙaunar yawanci za tă yi sanyi,
13 But he that endures to the end, shall be saved:
amma duk wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
14 and this gospel of the kingdom of heaven shall be preached in all the world, for a testimony to all the nations; and then shall the end come.
Za a kuma yi wa’azin wannan bisharar mulki a cikin dukan duniya, yă zama shaida ga dukan al’ummai, sa’an nan ƙarshen yă zo.
15 When therefore ye shall see the desolating abomination, spoken of by Daniel the prophet, standing at the holy place, (let him, that readeth, attend) then let those in Judea flee to the mountains:
“Saboda haka sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama mai kawo hallaka,’wanda annabi Daniyel ya yi magana a kai, yana tsaye a tsattsarkan wuri (mai karatu yă gane),
16 let not him that is at the top of the house come down into it,
to, sai waɗanda suke cikin Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu.
17 to take any thing out of his house;
Kada wani da yake a kan rufin gidansa, yă sauko don ɗaukar wani abu a gida.
18 nor let him that is in the field return back to take his clothes.
Kada wani da yake gona kuma yă komo don ɗaukar rigarsa.
19 But wo to them that are with child, and to them that give suck, in those days.
Kaiton mata masu ciki da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
20 Pray that your flight be not in the winter, nor on the sabbath:
Ku yi addu’a, kada gudunku yă zama a lokacin sanyi ko a ranar Asabbaci.
21 for there shall be then great affliction, such as has not been from the beginning of the world unto this time, no, nor ever shall be.
Gama a lokacin za a yi wata matsananciyar wahala, wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu ba kuwa za a ƙara yi ba.
22 And unless those days be shortened, no one would be saved; but for the sake of the elect those days shall be shortened.
“Da ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da babu wani da zai tsira, amma saboda zaɓaɓɓun nan, za a taƙaita kwanakin.
23 Then if any shall say to you, Behold here is the Messiah, or there; believe it not:
A lokacin in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko, ‘Ga shi can!’ Kada ku gaskata.
24 for there shall rise up false Christs, and false prophets, who shall shew great signs and prodigies, so as to deceive, if possible, even the elect.
Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
25 Lo, I have told you before-hand: and therefore if they say to you,
Ga shi, na faɗa muku tun da wuri.
26 Behold, he is in the desert, go not out: behold, he is the secret chambers, believe them not:
“Saboda haka in wani ya ce muku, ‘Ga shi can a hamada,’ kada ku fita; ko, ‘Ga shi nan a ɗakunan ciki,’ kada ku gaskata.
27 for as the lightning cometh from the east, and flashes in an instant even to the west, so shall be the coming of the Son of man.
Gama kamar yadda walƙiya take wulgawa walai daga gabas zuwa yamma, haka dawowar Ɗan Mutum zai kasance.
28 For wheresoever the carcase is, there will the eagles be gathered together.
Duk inda mushe yake, can ungulai za su taru.
29 And immediately after the affliction of those days, the fun shall be darkened, and the moon shall not give it's light, and the stars shall fall from heaven, and the powers of the heavens shall be shaken:
“Nan da nan bayan tsabar wahalan nan “‘sai a duhunta rana, wata kuma ba zai ba da haskensa ba; taurari kuma za su fāffāɗi daga sararin sama, za a kuma girgiza abubuwan sararin sama.’
30 and then shall appear the sign of the Son of man in heaven, and then shall all the tribes of the land mourn, and they shall see the Son of man coming as on the clouds of heaven with power and great glory:
“A sa’an nan ne alamar dawowar Ɗan Mutum zai bayyana a sararin sama, dukan al’umman duniya kuwa za su yi kuka. Za su ga Ɗan Mutum yana zuwa kan gizagizan sararin sama, da iko da kuma ɗaukaka mai girma.
31 and He will send forth his messengers with a trumpet of a loud voice, and they shall gather his elect from the four winds, from one end of heaven to the other.
Zai kuwa aiki mala’ikunsa su busa ƙaho mai ƙara sosai, za su kuwa tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga wannan bangon duniya zuwa wancan.
32 Now learn a parable from the fig-tree: when it's branch is tender and bringeth forth leaves, ye know that summer is nigh;
“Yanzu fa, sai ku koyi wannan darasi daga itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi ganyayensa kuma suka toho, kun san damina ta kusa.
33 so ye also, when ye shall see all these things, know that it is near even at the doors.
Haka kuma, sa’ad da kun ga dukan waɗannan abubuwa, ku sani ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
34 Verily I tell you, this generation shall not pass away, till all these be fulfilled.
Gaskiya nake gaya muku, wannan zamani ba zai shuɗe ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
35 Heaven and earth shall pass away, but my words shall not pass away.
Sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za tă taɓa shuɗe ba.
36 But of THAT day and hour knoweth no one, not even the angels of heaven, but my Father only:
“Babu wanda ya san wannan rana ko sa’a, ko mala’ikun da suke sama ma, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai.
37 for as the days of Noah were, so shall be also the coming of the Son of man;
Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
38 for as in the days before the flood they were eating and drinking, marrying and giving in marriage, till the day that Noah entered into the ark,
Gama a kwanaki kafin ruwan tsufana, mutane sun yi ta ci, sun kuma yi ta sha, suna aure, suna kuma aurarwa, har zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi;
39 and knew not of it till the deluge came and took them all away; so shall be also the coming of the Son of man.
ba su kuwa san abin da yake faruwa ba sai da ruwan tsufana ya zo ya share su tas. Haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
40 Then there shall be two in the field, the one shall be taken and the other left:
Maza biyu za su kasance a gona; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
41 and two women grinding at the mill, one taken and one left.
Mata biyu za su kasance suna niƙa; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
42 Watch therefore, for ye know not at what hour your Lord cometh:
“Saboda haka sai ku zauna a faɗake, gama ba ku san a wace rana ce Ubangijinku zai zo ba.
43 but this ye know, that if the master of the house had known at what hour the thief would come, he would have watched, and would not have suffered his house to be broke open: therefore be ye also ready;
Ku dai gane wannan, da maigida ya san ko a wane lokaci ne da dare, ɓarawo zai zo, da sai yă zauna a faɗake yă kuma hana a shiga masa gida.
44 for the Son of man cometh at a time that ye think not of.
Saboda haka ku ma, sai ku zauna a faɗake, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku za tă ba.
45 Who then is the faithful and prudent servant, whom his lord hath set over his family to give them food in due season?
“Wane ne bawan nan mai aminci da kuma mai hikima, wanda maigida ya sa yă lura da bayi a cikin gidansa, yă riƙa ba su abinci a daidai lokaci?
46 blessed is that servant, whom his lord when he cometh shall find so employed:
Zai zama wa bawan nan da kyau in maigidan ya dawo ya same shi yana yin haka.
47 verily I tell you, that he will set him over his whole estate.
Gaskiya nake gaya muku, zai sa shi yă lura da dukan dukiyarsa.
48 But if that servant be wicked and say in his heart, my master delayeth his coming,
Amma in wannan bawa mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Maigidana ba zai dawo da wuri ba.’
49 and begin to beat his fellow-servants, and to revel with drunkards:
Sa’an nan yă fara dūkan’yan’uwansa bayi, yana ci yana kuma sha tare da mashaya.
50 the lord of that servant will come in a day when he doth not expect him, and in an hour which he knows not,
Maigidan wannan bawa zai dawo a ranar da bai yi tsammani ba, a sa’ar kuma da bai sani ba.
51 and will cut him asunder, and appoint him his portion with hypocrites: where there will be weeping and gnashing of teeth.
Maigidan zai farfasa masa jiki da bulala, yă kuma ba shi wuri tare da munafukai, inda za a yi kuka da cizon haƙora.

< Matthew 24 >