< Acts 4 >

1 And while they were speaking to the people, the priests, and the captain of the temple, and the sadducees came upon them,
Sai firistoci da shugaban masu gadin haikalin da kuma Sadukiyawa suka hauro wurin Bitrus da Yohanna yayinda suke cikin magana da mutane.
2 being vexed that they taught the people, and preached through Jesus the resurrection from the dead.
Sun damu ƙwarai da gaske domin manzannin suna koya wa mutane suna kuma shela a cikin Yesu cewa akwai tashin matattu.
3 And they laid hands on them, and put them into custody till the next day: for it was now evening.
Sai suka kama Bitrus da Yohanna, amma da yake yamma ta riga ta yi sai suka sa su cikin kurkuku sai kashegari.
4 But many of them who heard the word, believed: and the number of the men was about five thousand.
Amma da yawa da suka ji saƙon suka gaskata, yawan mutanen kuwa ya ƙaru ya kai wajen dubu biyar.
5 And on the morrow their rulers, and elders, and scribes were gathered together at Jerusalem:
Kashegari, sai masu mulki, dattawa da kuma malaman dokoki suka taru a Urushalima.
6 and with them Annas the high priest, and Caiaphas, and John, and Alexander, and as many as were of the kindred of the high priest.
Annas babban firist yana nan, haka ma Kayifas Yohanna, Alekzanda da kuma sauran mutanen da suke iyalin babban firist.
7 And when they had set them in the midst, they asked them, By what power, or in what name have ye done this?
Suka sa aka kawo Bitrus da Yohanna a gabansu suka kuma fara yin musu tambayoyi cewa, “Da wane iko ko da wane suna kuka yi wannan?”
8 Then Peter filled with the holy Spirit said unto them, Ye rulers of the people,
Sai Bitrus, cike da Ruhu Mai Tsarki ya ce musu, “Masu mulki da dattawan mutane!
9 and elders of Israel, if we are this day examined about the benefit done to the impotent man,
In ana tuhumarmu ne yau saboda alherin da aka yi wa gurgun nan da kuma yadda aka warkar da shi,
10 by what means he is cured, be it known to you all, and to all the people of Israel, that by the name of Jesus Christ of Nazareth, whom ye crucified, but whom God hath raised from the dead, even by Him doth this man stand here before you whole.
to, sai ku san wannan, ku da dukan mutanen Isra’ila cewa da sunan Yesu Kiristi Banazare, wanda kuka gicciye amma wanda Allah ya tasar daga matattu ne, wannan mutum yake tsaye a gabanku lafiyayye.
11 This is the stone that was set at nought by you builders, which is become the head of the corner.
Shi ne, “‘dutsen da ku magina kuka ƙi, wanda kuwa ya zama dutsen kusurwar gini.’
12 And there is salvation in no other; for there is no other name under heaven given among men, by which we can be saved.
Ba a samun ceto ta wurin wani dabam, gama babu wani suna a ƙarƙashin sama da aka ba wa mutane wanda ta wurinsa dole mu sami ceto.”
13 Now when they saw the boldness of Peter and John, and perceived that they were plain and illiterate men, they were amazed; and they knew them again that they had been with Jesus:
Da suka ga ƙarfin halin Bitrus da Yohanna suka kuma gane cewa su marasa ilimi ne, talakawa kuma, sai suka yi mamaki suka kuma lura cewa waɗannan mutane sun kasance tare da Yesu.
14 but seeing the man that was cured standing with them, they had nothing to say against it.
Amma da yake sun ga mutumin da aka warkar yana tsaye a wurin tare da su, sai suka rasa abin faɗi.
15 Therefore they ordered them to withdraw from the council,
Saboda haka suka umarta a fitar da su daga Majalisar, sa’an nan suka yi shawara da juna.
16 and conferred among themselves, saying, What shall we do with these men? for that indeed an evident miracle hath been wrought by them is manifest to all the inhabitants of Jerusalem, and we cannot deny it.
Suka ce, “Me za mu yi da waɗannan mutane? Kowa da yake zama a Urushalima ya san sun yi abin banmamaki, kuma ba za mu iya yin mūsu wannan ba.
17 But that it may spread no farther among the people, let us severely charge them to speak no more to any man in this name.
Amma don a hana wannan abu daga ƙara bazuwa cikin mutane, dole mu kwaɓe mutanen nan kada su ƙara yi wa kowa magana cikin wannan suna.”
18 So they called them and commanded them not to speak at all, nor teach in the name of Jesus.
Sai suka sāke kiransu ciki suka kuma umarce su kada su kuskura su yi magana ko su ƙara koyarwa a cikin sunan Yesu.
19 But Peter and John answered them, and said, Whether it be right in the sight of God to obey you rather than God, judge ye:
Amma Bitrus da Yohanna suka amsa, “Ku shari’anta da kanku ko daidai ne a gaban Allah mu yi muku biyayya maimakon Allah.
20 for we cannot but speak the things which we have seen and heard.
Gama ba za mu iya daina yin magana game da abin da muka gani muka kuma ji ba.”
21 So they threatened them more severely, and let them go; not finding how to punish them, because of the people: for they all glorified God for that which was done.
Bayan ƙarin barazana sai suka bar su su tafi. Ba su iya yanke shawara yadda za a hore su ba, domin dukan mutane suna yabon Allah saboda abin da ya faru.
22 For the man was above forty years old, on whom this miraculous cure was wrought.
Gama mutumin da ya sami warkarwar banmamaki, shekarunsa sun fi arba’in.
23 Being dismissed they went to their own company, and reported all that the chief priests and elders had said to them.
Da aka sake su, Bitrus da Yohanna suka koma wajen mutanensu suka ba da labarin duk abin da manyan firistoci da dattawa suka faɗa musu.
24 And when they heard it, they lifted up their voice to God with one accord, and said, Lord, Thou art God, who hast made heaven and earth, and sea, and all things therein:
Sa’ad da suka ji wannan, sai suka ɗaga muryoyinsu gaba ɗaya cikin addu’a ga Allah, suka ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai ka halicci sama da ƙasa da kuma teku, da kome da yake cikinsu.
25 who by the mouth of thy servant David hast said, Why did the heathen rage, and the people imagine vain things?
Ka yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki ta bakin bawanka, kakanmu Dawuda cewa, “‘Don me ƙasashe suke fushi, mutane kuma suke ƙulla shawara a banza?
26 The kings of the earth set themselves, and the rulers were gathered together against the Lord and against his anointed.
Sarakunan duniya sun ja dāgā, masu mulki kuma sun taru gaba ɗaya, suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.’
27 For of a truth both Herod and Pontius Pilate, the Gentiles and the people of Israel, combined against thy holy child Jesus,
Tabbatacce Hiridus da Buntus Bilatus suka haɗu tare da Al’ummai da kuma mutanen Isra’ila a wannan birni ce don su ƙulla gāba da bawanka mai tsarki Yesu, wanda ka shafe.
28 (whom Thou hast anointed, ) to do whatever thy hand and thy counsel had before determined to be done.
Sun aikata abin da ikonka da kuma nufinka ya riga ya shirya tuntuni zai faru.
29 And now, Lord, behold their threatenings; and give unto thy servants to speak thy word with all freedom, while Thou art stretching forth thy hand to heal,
Yanzu, Ubangiji, ka dubi barazanansu ka kuma sa bayinka su furta maganarka da iyakar ƙarfin hali.
30 and while signs and wonders are done by the name of thy holy child Jesus.
Ka miƙa hannunka don ka warkar ka kuma yi ayyukan banmamaki da alamu masu banmamaki ta wurin sunan bawanka mai tsarki Yesu.”
31 And when they had prayed, the place in which they were assembled was shaken; and they were all filled with the holy Spirit, and they spake the word of God with freedom.
Bayan suka yi addu’a, sai inda suka taru ya jijjigu. Dukansu kuwa suka cika da Ruhu Mai Tsarki, suka yi ta shaidar maganar Allah babu tsoro.
32 And the heart and soul of the multitude that believed was one: no one called any of his possessions his own property, but they had all things common.
Dukan masu bi kuwa zuciyarsu ɗaya ne, nufinsu kuwa ɗaya. Babu wani da ya ce abin da ya mallaka nasa ne, amma sun raba kome da suke da shi.
33 And with great power did the apostles give their testimony of the resurrection of the Lord Jesus: and great grace was upon them all.
Da iko mai ƙarfi manzanni suka ci gaba da shaidar tashin matattu na Ubangiji Yesu, alheri mai yawa kuwa yana bisansu duka.
34 Neither was there any indigent person among them; for as many as were proprietors of lands or houses, sold them and brought the prices of what were sold,
Babu mabukata a cikinsu. Lokaci-lokaci waɗanda suke da gonaki ko gidaje sukan sayar da su, su kawo kuɗi daga abin da suka sayar,
35 and laid them at the apostles feet; and distribution was made to every one according to their necessity.
su ajiye a sawun manzannin, a kuma raba wa kowa gwargwadon bukatarsa.
36 So Joses who was by the apostles sirnamed Barnabas, which is a son of consolation,
Yusuf, wani Balawe daga Saifurus, wanda manzanni suke kira Barnabas (wanda yake nufin Ɗan Ƙarfafawa)
37 a Levite, by birth a Cyprian, having an estate, sold it and brought the money, and laid it at the feet of the apostles.
ya sayar da wata gonar da ya mallaki ya kuma kawo kuɗin ya ajiye a sawun manzanni.

< Acts 4 >