< Acts 24 >
1 And after five days, the high-priest Ananias came down with the elders, and one Tertulius an orator, who appeared before the governor against Paul.
Bayan kwana biyar sai Ananiyas babban firist ya tafi Kaisariya tare da waɗansu daga cikin dattawa da kuma wani lauya mai suna Tertullus, suka kawo ƙararsu game da Bulus a gaban gwamna.
2 And when he was called, Tertullus began to accuse him, saying, "As by thee we enjoy much peace, and glorious things are done to this nation by thy prudent administration,
Sa’ad da aka shigo da Bulus, sai Tertullus ya shiga kai ƙararsa a gaban Felis yana cewa, “Mun daɗe muna zaman lafiya a ƙarƙashinka, hangen nesanka kuma ya kawo gyare-gyare a wannan ƙasa.
3 we acknowledge it upon all occasions and in all places, most noble Felix, with all thankfulness.
Ko’ina da kuma a kowace hanya, ya mafifici Felis, mun amince da wannan da godiya marar iyaka.
4 But that I may not trespass upon thee too far, I beg thou wouldst hear us a few words with thy wonted goodness.
Amma don kada in ƙara gajiyar da kai, ina roƙonka ka yi haƙuri ka saurari ɗan taƙaitaccen jawabinmu.
5 For having found this man a pestilent fellow, and a mover of sedition among all the Jews throughout the world, and a ring-leader of the sect of the Nazarenes,
“Mun tarar da wannan mutum fitinanne ne, yana tā-da-na-zaune-tsaye a tsakanin Yahudawa ko’ina a duniya. Shi shugaban ɗarikar Nazarawa
6 and attempting to profane the temple, we apprehended him, and would have judged him according to our law.
har ma ya yi ƙoƙari ya ƙazantar da haikali; shi ya sa muka kama shi.
7 But Lysias the tribune came upon us, and with great violence took him away out of our hands, commanding his accusers to come unto thee:
8 from whom thou mayst thyself by examining him come to the knowledge of all these things of which we accuse him."
Ta wurin bincika shi da kanka za ka gane gaskiyar game da dukan waɗannan zargin da muke kawo a kansa.”
9 And the Jews also assented, saying, that these things were so.
Yahudawa ma suka goyi bayan zargin, suna tabbatar cewa waɗannan abubuwa haka suke.
10 Then Paul, when the governor permitted him to speak, answered in this manner, "As I know that thou hast been many years a judge to this nation, I do the more chearfully answer for myself:
Da gwamna ya yi masa alama yă yi magana, sai Bulus ya amsa ya ce, “Na san cewa ka yi shekaru da yawa kana mulki a wannan ƙasa; saboda haka ina farin ciki in kāre kaina.
11 because thou mayst know, that there are not more than twelve days since I went up to worship at Jerusalem:
Da sauƙi za ka iya tabbatar cewa, bai fi kwana goma sha biyu da suka wuce ne na tafi Urushalima, domin yin sujada ba.
12 and they neither found me disputing with any one in the temple, or making sedition among the people, neither in the synagogues, nor in the city:
Masu zargina ba su same ni ina gardama da kowa a haikali, ko kuma ina tā da hankalin jama’a a majami’u ko kuwa wani wuri dabam a cikin birni ba.
13 nor can they prove the things of which they now accuse me.
Ba kuwa za su iya tabbatar maka ƙarar da suke yi yanzu a kaina ba.
14 But this I confess unto thee, that after the way, which they call heresy, so do I worship the God of my fathers, believing all things which are written in the law, and the prophets:
Amma na yarda cewa ina bauta wa Allah na kakanninmu a matsayin mai bin Hanyar da suke kira ɗarika. Na gaskata dukan abin da ya amince da Doka da yake kuma a rubuce cikin Annabawa,
15 having hope in God, (which they themselves also expect) that there shall be a resurrection of the dead, both of the just and unjust.
ina kuma da irin bege ɗaya ga Allah yadda mutanen nan suke da shi, cewa akwai tashin matattu masu adalci da masu mugunta duka.
16 And on this account do I exercise myself, to have always a conscience void of offence both towards God and towards men.
Saboda haka, ina ƙoƙari kullum in kasance da lamiri mai tsabta a gaban Allah da mutane.
17 Now after several years I came to bring alms to my nation, and offerings.
“Bayan’yan shekaru da dama da ba na nan, sai na dawo Urushalima don in kawo wa mutanena kyautai saboda matalauta in kuma yi sadaka.
18 Upon which some Jews from Asia found me purified in the temple, neither with multitude nor with tumult:
Ni tsarkake ne sa’ad da suka same ni cikin filin haikalin ina yin haka. Babu taro tare da ni, ba kuwa ina tā da hankali ba.
19 who ought to have been here before thee, and make good their charge, if they had any thing against me.
Amma akwai waɗansu Yahudawa daga lardin Asiya, waɗanda ya kamata suna a nan a gabanka su kawo ƙara in suna da wani a kaina.
20 Or let these themselves say, if they found any crime in me, when I stood before the sanhedrim;
Ko kuwa waɗannan da suke a nan su faɗi laifin da suka same ni da shi sa’ad da na tsaya a gaban Majalisa,
21 unless for this one expression, that I cried out when I stood among them, For the resurrection of the dead I am called in question by you this day."
sai ko wannan abu ɗaya kaɗai da na ɗaga murya na faɗi yayinda nake tsaye a gabansu cewa, ‘A game da tashin matattu ake mini shari’a a gabanku yau.’”
22 And when Felix heard these things he put them off, (for he had been more particularly informed concerning this way of religion, ) and said, When Lysias the tribune comes down, I will thoroughly examine your matters.
Sai Felis, wanda yake da cikakken sani game da Hanyar, ya ɗaga sauraron ƙarar. Ya ce, “In Lisiyas shugaban ƙungiyar soja ya iso, zan yanke muku shari’a.”
23 And he commanded the centurion to keep Paul secure, and to let him have some liberty, and to hinder none of his friends from assisting him or coming to him.
Ya yi wa jarumin umarni yă tsare Bulus amma yă ba shi’yanci yă kuma bar abokansa su lura da bukatunsa.
24 Some days after Felix coming with his wife Drusilla, a Jewess, sent for Paul, and heard him concerning faith in Christ.
Bayan’yan kwanaki da dama sai Felis ya zo da matarsa Durusilla, mutuniyar Yahuda. Sai ya aika a zo da Bulus ya kuma saurare shi da yake magana game da bangaskiya cikin Kiristi Yesu.
25 And as he was reasoning of justice, temperance, and a future judgement, Felix trembled, and said, Go thy way for this time, and I will take a proper opportunity to call for thee again.
Da Bulus ya ci gaba jawabi a kan adalci, kamunkai da kuma hukunci mai zuwa, sai Felis ya tsorata ya ce, “Yanzu kam, ya isa haka! Kana iya tafi. In na sami zarafi, zan kira ka.”
26 And hoping also that money would be given him by Paul, that he might discharge him; he sent for him the more frequently, and conversed with him.
A wani fanni yana sa rai cewa Bulus zai ba shi toshiyar baki, saboda haka ya yi ta aika a kira masa Bulus yă yi magana da shi.
27 But after two years Felix received a successor, Porcius Festus; and being willing to gain favor with the Jews lest Paul confined.
Da shekaru biyu suka wuce, sai Forsiyus Festus, ya gāji Felis, amma domin Felis ya so yă biya wa Yahudawa bukata, sai ya bar Bulus a kurkuku.