< Acts 1 >
1 The former treatise, O Theophilus, I made concerning all that Jesus undertook both to do and to teach;
A littafina na farko, Tiyofilus, na rubuta game da dukan abin da Yesu ya fara yi, da abin da ya koyar
2 till the day in which He was taken up, after He had by the holy Spirit given instructions to the apostles whom He had chosen:
har zuwa ranar da aka ɗauke shi zuwa sama, bayan ya ba da umarnai ta wurin Ruhu Mai Tsarki ga manzannin da ya zaɓa.
3 to whom also He presented Himself alive, after He had suffered, by many certain proofs; being seen among them for forty days, and speaking of the things relating to the kingdom of God.
Bayan wahalarsa, ya bayyana kansa ga waɗannan mutane ya kuma ba da tabbatattun alamu masu yawa cewa yana da rai. Ya bayyana a gare su har kwana arba’in ya kuma yi musu magana game da mulkin Allah.
4 And meeting them together He commanded them not to depart from Jerusalem, but to wait for the promise of the Father, which, said He, ye have heard from me;
A wani lokaci, yayinda yake ci tare da su, ya ba su wannan umarni, “Kada ku bar Urushalima, amma ku jira kyautar da Ubana ya yi alkawari, wadda kuka ji na yi magana a kai.
5 for John indeed baptized with water, but ye shall within a few days be baptized with the holy Spirit.
Gama Yohanna ya yi baftisma daruwa, amma a cikin’yan kwanaki za a yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
6 Being therefore come together they asked Him, saying, Lord, wilt thou at this time restore the kingdom to Israel?
Saboda haka, sa’ad da suka taru, sai suka tambaye shi, “Ubangiji, a wannan lokaci za ka mayar da mulki ga Isra’ila?”
7 And He said unto them, It is not for you to know the times or seasons, which the Father hath reserved in his own power.
Ya ce musu, “Ba naku ba ne ku san lokuta ko ranakun da Uban ya shirya cikin ikonsa.
8 But ye shall receive power from the holy Spirit coming upon you: and ye shall be my witnesses both in Jerusalem, and in all Judea, and Samaria, and to the uttermost part of the earth.
Amma ku za ku karɓi iko sa’ad da Ruhu Mai Tsarki ya sauka a kanku; za ku kuma zama shaiduna cikin Urushalima, da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, zuwa kuma iyakar duniya.”
9 And having said these things, as they were looking upon Him, He was lifted up, and a cloud received Him out of their sight.
Bayan ya faɗi wannan, sai aka ɗauke shi sama a idanunsu sai wani girgije ya rufe shi daga ganinsu.
10 And while they were looking stedfastly toward heaven, as He went up, behold two men in white stood by them;
Suna zuba ido a bisa, zuwa cikin sararin sama yayinda yake tafiya, nan da nan, sai ga mutane biyu saye da fararen riguna tsaye kusa da su.
11 who said, Ye men of Galilee, why do ye stand gazing up to heaven? This Jesus who is taken up from you into heaven, shall so come in the manner ye have seen Him going into heaven.
Sai suka ce, “Mutanen Galili, don me kuke tsaye a nan kuna duban sararin sama? Wannan Yesu, wanda aka ɗauke daga gare ku zuwa sama, zai komo daidai yadda kuka ga ya tafi sama.”
12 Then they returned to Jerusalem from the mountain called Olivet, which is from Jerusalem a sabbath-day's journey.
Sai suka koma Urushalima daga tudun da ake kira Dutsen Zaitun, tafiyar ranar Asabbaci guda daga birnin.
13 And when they were come in to the city, they went up into an upper room, where Peter, and James, and John, and Andrew, Philip and Thomas, Bartholomew, and Matthew, James the son of Alpheus, and Simon the zealot, and Jude the brother of James, usually abode.
Da suka iso, sai suka hau gidan sama, zuwa ɗakin da suke zama. Waɗanda suka kasance kuwa su ne, Bitrus, Yohanna, Yaƙub da Andarawus; Filibus da Toma; Bartolomeyu da Mattiyu; Yaƙub ɗan Alfayus da Siman Zilot, da kuma Yahuda ɗan Yaƙub.
14 These all persevered with one accord in prayer and supplication with the women, and Mary the mother of Jesus, and his brethren.
Waɗannan duka suka duƙufa cikin addu’a, tare da waɗansu mata da Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma tare da’yan’uwansa.
15 And in these days Peter stood up in the midst of the disciples, (now the number of the persons that were together was about an hundred and twenty, )
A waɗancan kwanakin Bitrus ya miƙe tsaye cikin’yan’uwa masu bi (taron da ya yi kusan mutum ɗari da ashirin)
16 and said, Men and brethren, it was necessary that this scripture should be fulfilled, which the holy Ghost spake by the mouth of David, concerning Judas, who was guide to them that apprehended Jesus:
ya ce, “’Yan’uwana, dole a cika Nassin nan da Ruhu Mai Tsarki ya yi magana tun da daɗewa ta bakin Dawuda game da Yahuda, wanda ya zama jagora ga waɗanda suka kama Yesu
17 for he was numbered with us, and had obtained a part of this ministry.
dā shi ɗaya ne cikinmu, ya kuma yi hidima a cikin aikin nan.”
18 (Now this man purchased a field with the reward of iniquity; and falling down on his face, burst asunder in the middle, and all his bowels gushed out:
(Da ladar da ya samu saboda muguntarsa Yahuda ya sayi wani fili; a can ya fāɗi da kā, jikinsa ya fashe, hanjinsa kuma duk suka zubo.
19 (and it was known to all the inhabitants of Jerusalem, so that the field is called in their own dialect, Aceldama, that is, the field of blood: )
Kowa a Urushalima ya ji game da wannan, saboda haka suka kira wannan filin Akeldama, da yarensu, wato, Filin Jini.)
20 for it is written in the book of Psalms, Let his habitation be desolate, and let none dwell in it; and again, Let another take his office.)
Bitrus ya ce, “Gama yana a rubuce a cikin Littafin Zabura cewa, “‘Bari wurinsa yă zama babu kowa; kada kowa ya zauna a cikinsa,’ kuma, “‘Bari wani ya ɗauki matsayinsa na shugabanci.’
21 Wherefore it is necessary that one of these men, who have been conversant with us all the time that the Lord Jesus came in and out among us,
Saboda haka dole a zaɓi ɗaya daga cikin mutanen da suke tare da mu duk lokacin da Ubangiji Yesu yake shiga da fita a cikinmu,
22 from the baptism of John, till the day that He was taken up from us, should be joined with us as a witness of his resurrection.
farawa daga baftisma ta Yohanna har zuwa sa’ad da aka ɗauke Yesu daga gare mu. Gama dole ɗaya daga waɗannan ya zama shaidar tashinsa daga matattu tare da mu.”
23 And they proposed two, Joseph called Barsabas, who was surnamed Justus, and Matthias.
Saboda haka suka gabatar da mutane biyu. Yusuf mai suna Barsabbas (da aka kuma sani da Yustus) da kuma Mattiyas.
24 And they prayed and said, Thou, Lord, who knowest the hearts of all, shew us, which of these two Thou hast chosen,
Sai suka yi addu’a suka ce, “Ubangiji, ka san zuciyar kowa. Nuna mana wanne a cikin waɗannan biyu da ka zaɓa
25 to take part of this ministry and apostleship, from which Judas is fallen by his transgression, that he might go to his own place.
ya karɓi wannan aikin manzanci, wanda Yahuda ya bari don yă tafi wurin da yake nasa.”
26 And they gave out their lots, and the lot fell upon Matthias, and he was numbered with the apostles.
Sa’an nan suka jefa ƙuri’u, ƙuri’ar kuwa ta fāɗo a kan Mattiyas; sai aka sa shi cikin manzannin nan goma sha ɗaya.