< Matthew 27 >
1 Now when morning had come, all the chief priests and the elders of the people took counsel against Yeshua to put him to death.
Da gari ya waye, duk manyan firistoci da dattawan jama'a suka shirya yadda zasu kulla makirci domin su kashe shi.
2 They bound him, led him away, and delivered him up to Pontius Pilate, the governor.
Suka daure shi, suka mika shi ga gwamna Bilatus.
3 Then Judah, who betrayed him, when he saw that Yeshua was condemned, felt remorse, and brought back the thirty pieces of silver to the chief priests and elders,
Sa'adda Yahuza, wanda ya bashe shi, ya ga an zartarwa Yesu hukuncin kisa, ya nemi tuba ya kuma mayar da azurfar talatin ga manyan firistocin da dattawan,
4 saying, “I have sinned in that I betrayed innocent blood.” But they said, “What is that to us? You see to it.”
yace, “Na yi zunubi ta wurin cin amanar mara laifi.” Amma sukace, “Ina ruwan mu? Ka ji da shi da kanka?”
5 He threw down the pieces of silver in the sanctuary and departed. Then he went away and hanged himself.
Sai ya jefar da kwandalolin azurfar a kasa cikin haikalin ya kuma bar su, ya tafi ya rataye kansa.
6 The chief priests took the pieces of silver and said, “It’s not lawful to put them into the treasury, since it is the price of blood.”
Sai babban firist ya dauki kwandalolin azurfar ya ce, “Ba daidai bane bisa ga shari'a musa wannan cikin ma'aji, saboda kudin jini ne.”
7 They took counsel, and bought the potter’s field with them to bury strangers in.
Sai suka tattauna al'amarin a tsakanin su, kudin kuma suka sayi filin maginin tukwane domin makabatar baki.
8 Therefore that field has been called “The Field of Blood” to this day.
Dalilin wannan ne ake kiran wurin, “Filin jini” har yau.
9 Then that which was spoken through Jeremiah the prophet was fulfilled, saying, “They took the thirty pieces of silver, the price of him upon whom a price had been set, whom some of the children of Israel priced,
Sai abin da aka fada ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa, “Suka dauki tsabar azurfa talatin na farashin da mutanen Isra'ila suka sa a kansa,
10 and they gave them for the potter’s field, as the Lord commanded me.”
suka bayar domin sayen filin mai tukwane, kamar yadda Ubangiji ya umarce ni.”
11 Now Yeshua stood before the governor; and the governor asked him, saying, “Are you the King of the Jews?” Yeshua said to him, “So you say.”
Sai Yesu ya tsaya a gaban gwamna, gwamna ya kuma tambaye shi, “Kai sarkin Yahudawa ne?” Yesu ya amsa, “Haka ka fada.”
12 When he was accused by the chief priests and elders, he answered nothing.
Amma da manyan firistocin da dattawan suka zarge shi, bai ce komai ba.
13 Then Pilate said to him, “Don’t you hear how many things they testify against you?”
Sai Bilatus yace masa, “Baka ji dukan zarge-zargen da ake yi maka ba?”
14 He gave him no answer, not even one word, so that the governor marveled greatly.
Amma bai ce masa ko kalma guda ba, sai gwamna yayi matukar mamaki.
15 Now at the feast the governor was accustomed to release to the multitude one prisoner whom they desired.
To lokacin bikin idi, al'adar gwamna ne ya saki mutum guda wanda jama'a suka zaba.
16 They had then a notable prisoner called Barabbas.
A wannan lokacin suna da wani sanannen dan kurkuku mai suna Barabbas.
17 When therefore they were gathered together, Pilate said to them, “Whom do you want me to release to you? Barabbas, or Yeshua who is called Messiah?”
To da suka tattaru, sai Bilatus yace masu, “Wa kuke so a sakar maku? Barabbas, ko Yesu wanda ake kira Almasihu?”
18 For he knew that because of envy they had delivered him up.
Saboda ya san sun kawo shi ne domin kishi.
19 While he was sitting on the judgment seat, his wife sent to him, saying, “Have nothing to do with that righteous man, for I have suffered many things today in a dream because of him.”
Da yake zaune a kujerar shari'a, matarsa ta aika masa cewa, “Ka fita sha'anin mutumin nan marar laifi. Saboda na sha wahala sosai a yau cikin mafarki saboda shi.”
20 Now the chief priests and the elders persuaded the multitudes to ask for Barabbas and destroy Yeshua.
A lokacin nan manyan firistoci da dattawa suka rinjayi ra'ayin jama'a suce a sakar masu da Barabbas, a kashe Yesu.
21 But the governor answered them, “Which of the two do you want me to release to you?” They said, “Barabbas!”
Sai gwamna ya tambayesu, “Wa kuke so a sakar maku?” Sukace, “Barabbas.”
22 Pilate said to them, “What then shall I do to Yeshua who is called Messiah?” They all said to him, “Let him be crucified!”
Bilatus yace masu, “Me zan yi da Yesu wanda ake kira Almasihu?” Sai duka suka amsa, “A gicciye shi.”
23 But the governor said, “Why? What evil has he done?” But they cried out exceedingly, saying, “Let him be crucified!”
Sai yace, “Don me, wane laifi ya aikata?” Amma suka amsa da babbar murya, “A gicciye shi”
24 So when Pilate saw that nothing was being gained, but rather that a disturbance was starting, he took water and washed his hands before the multitude, saying, “I am innocent of the blood of this righteous person. You see to it.”
Amma da Bilatus ya ga ba zai iya komai ba don hargitsi zai iya barkewa, ya dauki ruwa ya wanke hannuwansa a gaban jama'a, yace, “Ba ni da laifi ga jinin mutumin nan marar laifi. Ku yi abin da kuka ga dama.”
25 All the people answered, “May his blood be on us and on our children!”
Duka mutanen sukace, “Bari jininsa ya kasance a kan mu da 'ya'yan mu.”
26 Then he released Barabbas to them, but Yeshua he flogged and delivered to be crucified.
Sai ya sakar masu da Barabbas amma yayi wa Yesu bulala ya mika shi garesu domin su gicciye shi.
27 Then the governor’s soldiers took Yeshua into the Praetorium, and gathered the whole garrison together against him.
Sai sojojin gwamna suka dauki Yesu zuwa farfajiya suka kuma tara dukan rundunar sojoji.
28 They stripped him and put a scarlet robe on him.
Suka yi masa tumbur sa'annan suka sa masa jar alkyabba.
29 They braided a crown of thorns and put it on his head, and a reed in his right hand; and they kneeled down before him and mocked him, saying, “Hail, King of the Jews!”
Sai suka yi masa rawanin kaya suka sa a kansa, suka kuma bashi sanda a hannunsa na dama. Suka rusuna a gabansa suna masa ba'a, suna cewa, “Ranka ya dade, Sarkin Yahudawa!”
30 They spat on him, and took the reed and struck him on the head.
Suka kuma tofa masa yawu, suka kwace sandar suka buga masa a ka.
31 When they had mocked him, they took the robe off him, and put his clothes on him, and led him away to crucify him.
Bayan sun gama masa ba'a, suka cire masa alkyabbar suka sa masa kayansa, suka jagorance shi zuwa wurin da za a gicciye shi.
32 As they came out, they found a man of Cyrene, Simon by name, and they compelled him to go with them, that he might carry his cross.
Da suka fito waje, sai suka iske wani Bakurame mai suna Saminu, wanda suka tilasta ya tafi tare dasu domin ya dauki gicciyen.
33 When they came to a place called “Golgotha”, that is to say, “The place of a skull,”
Suka iso wani wuri da ake kira Golgotta, wanda ke nufin,”Wurin kwalluwa.”
34 they gave him sour wine to drink mixed with gall. When he had tasted it, he would not drink.
Suka bashi ruwan inabi da aka gauraya da wani abu mai daci. Amma da ya 'dan-'dana shi sai ya ki sha.
35 When they had crucified him, they divided his clothing among them, casting lots,
Bayan da suka gicciye shi, suka kada kuri'a a kan rigarsa.
36 and they sat and watched him there.
Suka kuma zauna suna kallonsa.
37 They set up over his head the accusation against him written, “THIS IS YESHUA, THE KING OF THE JEWS.”
A sama da kansa suka sa abinda ake tuhumarsa da ita a rubuce, “Wannan shine sarkin Yahudawa.”
38 Then there were two robbers crucified with him, one on his right hand and one on the left.
An gicciye shi da 'yanfashi guda biyu, daya ta damansa dayan kuma ta hagunsa.
39 Those who passed by blasphemed him, wagging their heads
Wadanda suke wucewa suna zaginsa, suna girgiza kai,
40 and saying, “You who destroy the temple and build it in three days, save yourself! If you are the Son of God, come down from the cross!”
suna kuma cewa, “Kai da kace zaka rushe haikali ka kuma gina shi a kwana uku, ka ceci kanka mana! In dai kai Dan Allah ne, ka sauko daga gicciyen!”
41 Likewise the chief priests also mocking with the scribes, the Pharisees, and the elders, said,
Ta haka ma manyan firistocin suka rika yi masa ba'a, tare da marubuta da shugabannin, suna cewa,
42 “He saved others, but he can’t save himself. If he is the King of Israel, let him come down from the cross now, and we will believe in him.
“Ya ceci wasu amma ya kasa ceton kansa. Shi ne sarkin Isra'ila. Ya sauko mana daga kan gicciyen, sai mu ba da gaskiya gareshi.
43 He trusts in God. Let God deliver him now, if he wants him; for he said, ‘I am the Son of God.’”
Tun da ya yarda da Allah. Bari Allahn ya cece shi mana, saboda yace, “Ni dan Allah ne.”
44 The robbers also who were crucified with him cast on him the same reproach.
Hakan nan ma 'yanfashin guda biyu da aka gicciye su tare suka zage shi.
45 Now from the sixth hour there was darkness over all the land until the ninth hour.
To tun da tsakar rana sai duhu ya rufe kasar gaba daya har karfe uku na yamma.
46 About the ninth hour Yeshua cried with a loud voice, saying, “Eli, Eli, lima sabachthani?” That is, “My God, my God, why have you forsaken me?”
Wajen karfe uku, Yesu ya tada murya mai karfi yace, “Eli, Eli lama sabaktani?” wanda ke nufin, “Allahna, Allahna, don me ka yashe ni?”
47 Some of them who stood there, when they heard it, said, “This man is calling Elijah.”
Da wadanda suke tsaye kusa suka ji haka, sai sukace, “Yana kiran Iliya.”
48 Immediately one of them ran and took a sponge, filled it with vinegar, put it on a reed, and gave him a drink.
Nan take wani ya ruga da gudu ya dauki soso ya tsoma cikin ruwan inabi mai tsami ya soka kan sandar kara ya mika masa ya sha.
49 The rest said, “Let him be. Let’s see whether Elijah comes to save him.”
Sai sauran sukace, “Rabu da shi mu gani ko Iliya zai zo ya cece shi.”
50 Yeshua cried again with a loud voice, and yielded up his spirit.
Sai Yesu ya ta da murya mai karfi yayi kuka sai ya saki ruhunsa.
51 Behold, the veil of the temple was torn in two from the top to the bottom. The earth quaked and the rocks were split.
Sai labullen haikali ya yage gida biyu daga sama zuwa kasa. Kasa kuma ta girgiza, duwatsu suka farfashe.
52 The tombs were opened, and many bodies of the holy ones who had fallen asleep were raised;
Kaburbura suka bude, tsarkaka kuwa wadanda suke barci da yawa suka tashi.
53 and coming out of the tombs after his resurrection, they entered into the holy city and appeared to many.
Suka fito daga kaburbura bayan tashinsa, suka shiga birni mai tsarki suka bayyana ga mutane da yawa.
54 Now the centurion and those who were with him watching Yeshua, when they saw the earthquake and the things that were done, were terrified, saying, “Truly this was the Son of God!”
Da hafsan sojan da wadanda suke kallon Yesu suka ga girgizar kasar da abinda ya faru, suka ji tsoro kwarai sukace, “Hakika wannan Dan Allah ne”
55 Many women were there watching from afar, who had followed Yeshua from Galilee, serving him.
Mata dayawa da suka bi Yesu daga Galili domin su lura da shi suka tsaya suna kallo daga nesa.
56 Among them were Miriam Magdalene, Miriam the mother of Jacob and Yosi, and the mother of the sons of Zebedee.
A cikin su akwai Maryamu Magadaliya, Maryamu uwar Yesu da Yusufu, da uwar 'ya'yan Zabadi.
57 When evening had come, a rich man from Arimathaea named Joseph, who himself was also Yeshua’s disciple, came.
Da yamma sai wani attajiri mutumin Armatiya ya zo, mai suna Yusufu wanda shi ma almajirin Yesu ne.
58 This man went to Pilate and asked for Yeshua’s body. Then Pilate commanded the body to be given up.
Ya je wurin Bilatus ya roka a bashi jikin Yesu. Sai Bilatus ya umarta a bashi.
59 Joseph took the body and wrapped it in a clean linen cloth
Yusufu ya dauki jikin, ya rufe shi da likafani mai tsabta,
60 and laid it in his own new tomb, which he had cut out in the rock. Then he rolled a large stone against the door of the tomb, and departed.
sai ya sa shi a cikin sabon kabarinsa da ya sassaka cikin dutse. Sai ya mirgina babban dutse a bakin kofar kabarin ya tafi.
61 Miriam Magdalene was there, and the other Miriam, sitting opposite the tomb.
Maryamu Magadaliya da dayan Maryamun suna nan zaune akasin kabarin.
62 Now on the next day, which was the day after the Preparation Day, the chief priests and the Pharisees were gathered together to Pilate,
Washegari, wato bayan ranar Shiri, Sai manyan firistoci da Farisawa suka taru tare da Bilatus.
63 saying, “Sir, we remember what that deceiver said while he was still alive: ‘After three days I will rise again.’
Sukace, “Mai gida, mun tuna lokacin da mayaudarin nan yake da rai, yace, “Bayan kwana uku zan tashi.”
64 Command therefore that the tomb be made secure until the third day, lest perhaps his disciples come at night and steal him away, and tell the people, ‘He is risen from the dead;’ and the last deception will be worse than the first.”
Saboda haka, ka bada umarni a tsare kabarin na kwana uku. In ba haka ba almajiransa zasu zo su sace shi, kuma su ce wa mutane, “Ya tashi daga mattatu.” Kuma yaudarar karshe zata fi ta farko muni.”
65 Pilate said to them, “You have a guard. Go, make it as secure as you can.”
Bilatus yace masu, “Ku dauki masu tsaro. Kuyi tsaro iyakar karfin ku.”
66 So they went with the guard and made the tomb secure, sealing the stone.
Sai suka tafi suka tsare kabarin, suka hatimce dutsen, suka sa masu tsaro.