< Mark 13 >

1 As he went out of the temple, one of his disciples said to him, “Rabbi, see what kind of stones and what kind of buildings!”
da Yesu ke fita daga Haikalin, sai daya daga cikin almajirnsa ya ce masa “malam, dubi kyawawan duwatsunnan da kyawawan gine-ginnenan!”
2 Yeshua said to him, “Do you see these great buildings? There will not be left here one stone on another, which will not be thrown down.”
Ya ce masa, ka ga wadannan kyawawan gine- ginen? babu wani dutsen da za a bar shi akan dan'uwansa, da ba za a rushe shi ba.”
3 As he sat on the Mount of Olives opposite the temple, Peter, Jacob, Yochanan, and Andrew asked him privately,
Yana zaune a kan dutsen zaitun wanda yake kusa da Haikali, sai Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, da Andarawus suka tambaye shi a asirce, suka ce.
4 “Tell us, when will these things be? What is the sign that these things are all about to be fulfilled?”
Gaya mana yaushe za a yi wadannan abubuwa? mecece zata zama alamar faruwar wadanna abubuwa da zasu faru?''
5 Yeshua, answering, began to tell them, “Be careful that no one leads you astray.
Yesu ya ce masu, “ku kula, kada kowa ya rudeku.
6 For many will come in my name, saying, ‘I am he!’ and will lead many astray.
Da yawa za su zo da sunana, suna cewa nine shi, har su bad da mutane da yawa.
7 “When you hear of wars and rumors of wars, don’t be troubled. For those must happen, but the end is not yet.
In kuka ji labarin yake- yake, da jita-jitarsu kada ku damu, wannan zai faru, amma karshen duniya bai gabato ba.
8 For nation will rise against nation, and kingdom against kingdom. There will be earthquakes in various places. There will be famines and troubles. These things are the beginning of birth pains.
Al'umma za ta tasarwa al'umma, mulki ya tasarwa mulki. Za a yi girgizar kasa awurare dabam-dabam, da kuma yunwa, amma fa dukkan wadanna abubuwan mafarin azaba ne.
9 “But watch yourselves, for they will deliver you up to councils. You will be beaten in synagogues. You will stand before rulers and kings for my sake, for a testimony to them.
Amma, ku zauna a fadake. Don za su kai ku gaban majalisa. za a yi maku duka a cikin majami'u. Su kuma kai ku gaban masu mulki da sarakuna, saboda sunana, domin ku ba da shaida a gare su.
10 The Good News must first be preached to all the nations.
Amma lallai sai an fara yi wa dukkan al, ummai bishara.
11 When they lead you away and deliver you up, don’t be anxious beforehand or premeditate what you will say, but say whatever will be given you in that hour. For it is not you who speak, but the Holy Spirit.
Sa'ad da suka kai ku gaban shari'a suka mika ku, kada ku damu a wannan lokacin, za a baku abin da zaku fada, Amma duk abin da aka yi muku a wannn lokacin, shi za ku fada, domin ba ku ne kuke magana ba, Ruhu mai tsarki ne.
12 “Brother will deliver up brother to death, and the father his child. Children will rise up against parents and cause them to be put to death.
Dan'uwa zai bada dan'uwarsa akashe shi, uba kuwa dansa. Yara kuma zasu tayar wa iyayensu har su sa akashe su.
13 You will be hated by all men for my name’s sake, but he who endures to the end will be saved.
Za a ki ku saboda sunana, amma duk wanda ya jumre har karshe zai cetu.
14 “But when you see the abomination of desolation, spoken of by Daniel the prophet, standing where it ought not” (let the reader understand), “then let those who are in Judea flee to the mountains,
Sa'adda kuka ga an kafa mummunan aikin sabo mai ban kyama a wurin da bai kamata ba (bari mai karatu ya fahimta), to, bari wadanda suke kasar Yahudiya, su gudu zuwa dutse.
15 and let him who is on the housetop not go down, nor enter in, to take anything out of his house.
Wanda yake tudu kuma kada ya sauko ya shiga gida garin daukar wani abu.
16 Let him who is in the field not return back to take his cloak.
Wanda yake gona kuma kada ya koma garin daukar mayafinsa.
17 But woe to those who are with child and to those who nurse babies in those days!
Amma, kaiton masu juna biyu da masu goyo a wannan lokacin.
18 Pray that your flight won’t be in the winter.
Ku yi addu, a kada abin ya faru da damina.
19 For in those days there will be oppression, such as there has not been the like from the beginning of the creation which God created until now, and never will be.
A lokacin za ayi wata matsanaciyar wahala, wadda bata taba faruwa ba, tun farkon halittar da Allah ya yi har zuwa yau, ba kuwa za a taba yi ba har abada.
20 Unless the Lord had shortened the days, no flesh would have been saved; but for the sake of the chosen ones, whom he picked out, he shortened the days.
In da ba ubangiji ya rage kwanakin nan ba, da ba Dan adam din zai tsira. Amma saboda zabbabunan da ya zaba, ya rage kwanakin.
21 Then if anyone tells you, ‘Look, here is the Messiah!’ or, ‘Look, there!’ don’t believe it.
To, in wani ya ce maku, kun ga Almasihu nan!' ko, 'kun gan shi can, kada ku gaskata.
22 For false messiahs and false prophets will arise and will show signs and wonders, that they may lead astray, if possible, even the chosen ones.
Gama almasihan karya, da annabawan karya zasu bayyana kuma, zasu yi abubuwan al'ajibai masu ban mamaki.
23 But you watch. “Behold, I have told you all things beforehand.
Amma ku zauna a fadake, Na dai fada maku wadannan abubuwan kafin lokacin.
24 But in those days, after that oppression, the sun will be darkened, the moon will not give its light,
Amma, bayan matsanaciyar wahalannan, rana zata duhunta, wata kuma ba zai bada haske ba.
25 the stars will be falling from the sky, and the powers that are in the heavens will be shaken.
Taurari za su fado daga sararin sama, za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama.
26 Then they will see the Son of Man coming in clouds with great power and glory.
Sa' annan zasu ga Dan mutum na zuwa a cikin gajimare, da iko mai girma da daukaka.
27 Then he will send out his angels, and will gather together his chosen ones from the four winds, from the ends of the earth to the ends of the sky.
Zai aiko da mala'ikunsa su tattaro zabbabunsa daga kusuwoyi hudu na duniya(watau Gabas da Yamma, kudu da Arewa) har zuwa karshen sama.
28 “Now from the fig tree, learn this parable. When the branch has now become tender and produces its leaves, you know that the summer is near;
“Ku yi koyi da itacen baure. Da zarar rassansa sun fara taushi yana kuma fitar da toho, kun san damina ta yi kusa ke nan.
29 even so you also, when you see these things coming to pass, know that it is near, at the doors.
Sa'adda kuka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku dai sani ya kusato, a bakin kofa ma ya ke.
30 Most certainly I say to you, this generation will not pass away until all these things happen.
Hakika ina gaya maku, zamanin nan ba zai shude ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
31 Heaven and earth will pass away, but my words will not pass away.
Sararin sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
32 “But of that day or that hour no one knows—not even the angels in heaven, nor the Son, but only the Father.
Amma wannan rana ko sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun sama, ko Dan, sai dai Uban kadai.
33 Watch, keep alert, and pray; for you don’t know when the time is.
Ku kula, ku zauna a fadake, kuna addu'a don baku san ranar da lokacin zai yi ba.
34 “It is like a man traveling to another country, having left his house and given authority to his servants, and to each one his work, and also commanded the doorkeeper to keep watch.
Kamar yadda mutum mai tafiya, in ya bar gida ya wakilta bayinsa kan gidansa, kowanne da aikinsa, ya kuma umarci mai gadi ya zauna a fadake.
35 Watch therefore, for you don’t know when the lord of the house is coming—whether at evening, or at midnight, or when the rooster crows, or in the morning;
To, ku zauna a fadake don ba ku san lokacin da maigidan zai zo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko da carar zakara ne, ko da safe ne.
36 lest, coming suddenly, he might find you sleeping.
Kada ya zo ba zato, ya samu kuna barci.
37 What I tell you, I tell all: Watch!”
Abinda na gaya maku, ina gaya wa kowa, shine ku zauna a fadake!”

< Mark 13 >