< Psalms 44 >
1 For the Chief Musician. By the sons of Korah. A contemplative psalm. We have heard with our ears, God; our fathers have told us what work you did in their days, in the days of old.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
2 You drove out the nations with your hand, but you planted them. You afflicted the peoples, but you spread them abroad.
Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
3 For they didn’t get the land in possession by their own sword, neither did their own arm save them; but your right hand, your arm, and the light of your face, because you were favourable to them.
Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
4 God, you are my King. Command victories for Jacob!
Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
5 Through you, we will push down our adversaries. Through your name, we will tread down those who rise up against us.
Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
6 For I will not trust in my bow, neither will my sword save me.
Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
7 But you have saved us from our adversaries, and have shamed those who hate us.
amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
8 In God we have made our boast all day long. We will give thanks to your name forever. (Selah)
A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
9 But now you rejected us, and brought us to dishonour, and don’t go out with our armies.
Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
10 You make us turn back from the adversary. Those who hate us take plunder for themselves.
Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
11 You have made us like sheep for food, and have scattered us amongst the nations.
Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
12 You sell your people for nothing, and have gained nothing from their sale.
Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
13 You make us a reproach to our neighbours, a scoffing and a derision to those who are around us.
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
14 You make us a byword amongst the nations, a shaking of the head amongst the peoples.
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
15 All day long my dishonour is before me, and shame covers my face,
Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
16 at the taunt of one who reproaches and verbally abuses, because of the enemy and the avenger.
saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
17 All this has come on us, yet we haven’t forgotten you. We haven’t been false to your covenant.
Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
18 Our heart has not turned back, neither have our steps strayed from your path,
Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
19 though you have crushed us in the haunt of jackals, and covered us with the shadow of death.
Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
20 If we have forgotten the name of our God, or spread out our hands to a strange god,
Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
21 won’t God search this out? For he knows the secrets of the heart.
da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
22 Yes, for your sake we are killed all day long. We are regarded as sheep for the slaughter.
Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
23 Wake up! Why do you sleep, Lord? Arise! Don’t reject us forever.
Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
24 Why do you hide your face, and forget our affliction and our oppression?
Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
25 For our soul is bowed down to the dust. Our body clings to the earth.
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
26 Rise up to help us. Redeem us for your loving kindness’ sake.
Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.