< Psalms 115 >

1 Not to us, LORD, not to us, but to your name give glory, for your loving kindness, and for your truth’s sake.
Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
2 Why should the nations say, “Where is their God, now?”
Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
3 But our God is in the heavens. He does whatever he pleases.
Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
4 Their idols are silver and gold, the work of men’s hands.
Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
5 They have mouths, but they don’t speak. They have eyes, but they don’t see.
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
6 They have ears, but they don’t hear. They have noses, but they don’t smell.
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
7 They have hands, but they don’t feel. They have feet, but they don’t walk, neither do they speak through their throat.
suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
8 Those who make them will be like them; yes, everyone who trusts in them.
Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
9 Israel, trust in the LORD! He is their help and their shield.
Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
10 House of Aaron, trust in the LORD! He is their help and their shield.
Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
11 You who fear the LORD, trust in the LORD! He is their help and their shield.
Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
12 The LORD remembers us. He will bless us. He will bless the house of Israel. He will bless the house of Aaron.
Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
13 He will bless those who fear the LORD, both small and great.
zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
14 May the LORD increase you more and more, you and your children.
Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
15 Blessed are you by the LORD, who made heaven and earth.
Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
16 The heavens are the LORD’s heavens, but he has given the earth to the children of men.
Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
17 The dead don’t praise the LORD, nor any who go down into silence,
Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
18 but we will bless the LORD, from this time forward and forever more. Praise the LORD!
mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.

< Psalms 115 >