< Numbers 26 >

1 After the plague, the LORD spoke to Moses and to Eleazar the son of Aaron the priest, saying,
Bayan annobar, sai Ubangiji ya yi magana da Musa da Eleyazar ɗan Haruna, firist ya ce,
2 “Take a census of all the congregation of the children of Israel, from twenty years old and upward, by their fathers’ houses, all who are able to go out to war in Israel.”
“Ku ƙidaya dukan jama’ar Isra’ila daga mai shekaru ashirin zuwa gaba da za su iya aikin sojan Isra’ila.”
3 Moses and Eleazar the priest spoke with them in the plains of Moab by the Jordan at Jericho, saying,
Musa da Eleyazar firist suka yi musu magana a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko, suka ce,
4 “Take a census, from twenty years old and upward, as the LORD commanded Moses and the children of Israel.” These are those who came out of the land of Egypt.
“Ku ƙidaya maza daga mai shekara ashirin zuwa gaba yadda Ubangiji ya umarci Musa.” Waɗannan su ne Isra’ilawan da suka fito daga Masar.
5 Reuben, the firstborn of Israel; the sons of Reuben: of Hanoch, the family of the Hanochites; of Pallu, the family of the Palluites;
Zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila, daga Hanok; kabilar Hanokawa; daga Fallu; kabilar Falluyawa;
6 of Hezron, the family of the Hezronites; of Carmi, the family of the Carmites.
daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Karmi, kabilar Karmiyawa.
7 These are the families of the Reubenites; and those who were counted of them were forty-three thousand and seven hundred and thirty.
Waɗannan su ne kabilan Ruben; jimillarsu ta kai 43,730.
8 The son of Pallu: Eliab.
Ɗan Fallu kuwa shi ne Eliyab,
9 The sons of Eliab: Nemuel, Dathan, and Abiram. These are that Dathan and Abiram who were called by the congregation, who rebelled against Moses and against Aaron in the company of Korah when they rebelled against the LORD;
’ya’yan Eliyab maza kuwa su ne, Nemuwel, Datan da Abiram. Datan da Abiram nan, su ne shugabannin mutanen da suka tayar wa Musa da Haruna, suna kuma cikin waɗanda suka bi Kora sa’ad da ya tayar wa Ubangiji.
10 and the earth opened its mouth, and swallowed them up together with Korah when that company died; at the time the fire devoured two hundred and fifty men, and they became a sign.
Ƙasa kuwa ta buɗe ta haɗiye su tare da Kora, wanda ƙungiyarsa ta mutu sa’ad da wuta ta cinye mutum 250. Wannan kuwa ya zama alamar faɗakarwa.
11 Notwithstanding, the sons of Korah didn’t die.
Amma fa, zuriyar Kora ba tă mutu ba.
12 The sons of Simeon after their families: of Nemuel, the family of the Nemuelites; of Jamin, the family of the Jaminites; of Jachin, the family of the Jachinites;
Zuriyar Simeyon bisa ga kabilansu, daga Nemuwel, kabilar Nemuwelawa; daga Yamin, kabilar Yaminawa; daga Yakin, kabilar Yakinawa;
13 of Zerah, the family of the Zerahites; of Shaul, the family of the Shaulites.
daga Zera, kabilar Zerawa; daga Sha’ul, kabilar Sha’ul.
14 These are the families of the Simeonites, twenty-two thousand and two hundred.
Waɗannan su ne kabilan Simeyon; jimillarsu ta kai 22,200.
15 The sons of Gad after their families: of Zephon, the family of the Zephonites; of Haggi, the family of the Haggites; of Shuni, the family of the Shunites;
Zuriyar Gad bisa ga kabilansu, daga Zafon, kabilar Zafonawa; daga Haggi, kabilar Haggiwa; daga Shuni, kabilar Shunawa;
16 of Ozni, the family of the Oznites; of Eri, the family of the Erites;
daga Ozni, kabilar Ozniyawa daga Eri, kabilar Eriyawa;
17 of Arod, the family of the Arodites; of Areli, the family of the Arelites.
daga Arod, kabilar Arodiyawa; daga Areli, kabilar Areliyawa.
18 These are the families of the sons of Gad according to those who were counted of them, forty thousand and five hundred.
Waɗannan su ne kabilan Gad, jimillarsu ta kai 40,500.
19 The sons of Judah: Er and Onan. Er and Onan died in the land of Canaan.
Er da Onan,’ya’yan Yahuda ne, amma sun mutu a Kan’ana.
20 The sons of Judah after their families were: of Shelah, the family of the Shelanites; of Perez, the family of the Perezites; of Zerah, the family of the Zerahites.
Zuriyar Yahuda bisa ga kabilansu, daga Shela, kabilar Shelayawa daga Ferez, kabilar Ferezawa; daga Zera, kabilar Zerawa;
21 The sons of Perez were: of Hezron, the family of the Hezronites; of Hamul, the family of the Hamulites.
Zuriyar Ferez kuwa, daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Hamul; kabilar Hamulawa.
22 These are the families of Judah according to those who were counted of them, seventy-six thousand and five hundred.
Waɗannan su ne kabilan Yahuda; jimillarsu ta kai 76,500.
23 The sons of Issachar after their families: of Tola, the family of the Tolaites; of Puvah, the family of the Punites;
Zuriyar Issakar bisa ga kabilansu, daga Tola, kabilar Tolatawa; daga Fuwa, kabilar Fuwayawa;
24 of Jashub, the family of the Jashubites; of Shimron, the family of the Shimronites.
daga Yashub, kabilar Yashubawa; daga Shimron, kabilar Shimronawa.
25 These are the families of Issachar according to those who were counted of them, sixty-four thousand and three hundred.
Waɗannan su ne kabilan Issakar; jimillarsu ta kai 64,300.
26 The sons of Zebulun after their families: of Sered, the family of the Seredites; of Elon, the family of the Elonites; of Jahleel, the family of the Jahleelites.
Zuriyar Zebulun bisa ga kabilansu, daga Sered, kabilar Seredawa; daga Elon kabilar Elonawa; daga Yaleyel; kabilar Yaleyewa.
27 These are the families of the Zebulunites according to those who were counted of them, sixty thousand and five hundred.
Waɗannan su ne kabilan Zebulun, jimillarsu ta kai 60,500.
28 The sons of Joseph after their families: Manasseh and Ephraim.
Zuriyar Yusuf bisa ga kabilansu ta wurin Manasse da Efraim.
29 The sons of Manasseh: of Machir, the family of the Machirites; and Machir became the father of Gilead; of Gilead, the family of the Gileadites.
Zuriyar Manasse, daga Makir, kabilar Makiriyawa (Makir shi ne mahaifin Gileyad); daga Gileyad, kabilar Gileyadawa.
30 These are the sons of Gilead: of Iezer, the family of the Iezerites; of Helek, the family of the Helekites;
Waɗannan su ne zuriya Gileyad, daga Iyezer, kabilar Iyezerawa; daga Helek, kabilar Helekawa;
31 and Asriel, the family of the Asrielites; and Shechem, the family of the Shechemites;
daga Asriyel, kabilar Asriyelawa; daga Shekem, kabilar Shekem;
32 and Shemida, the family of the Shemidaites; and Hepher, the family of the Hepherites.
daga Shemida, kabilar Shemadawa; daga Hefer, kabilar Heferawa.
33 Zelophehad the son of Hepher had no sons, but daughters: and the names of the daughters of Zelophehad were Mahlah, Noah, Hoglah, Milcah, and Tirzah.
(Zelofehad ɗan Hefer, ba shi da’ya’ya maza;’yan mata ne kaɗai ya haifa, sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.)
34 These are the families of Manasseh. Those who were counted of them were fifty-two thousand and seven hundred.
Waɗannan su ne kabilan Manasse, jimillarsu ta kai 52,700.
35 These are the sons of Ephraim after their families: of Shuthelah, the family of the Shuthelahites; of Becher, the family of the Becherites; of Tahan, the family of the Tahanites.
Waɗannan su ne kabilan Efraim bisa ga kabilansu, daga Shutela, kabilar Shutelawa; daga Beker, kabilar Bekerawa; daga Tahan, kabilar Tahanawa.
36 These are the sons of Shuthelah: of Eran, the family of the Eranites.
Waɗannan su ne kabilan Shutelawa, daga Eran, kabilar Eranawa.
37 These are the families of the sons of Ephraim according to those who were counted of them, thirty-two thousand and five hundred. These are the sons of Joseph after their families.
Waɗannan su ne kabilan Efraim; jimillarsu ta kai 32,500. Waɗannan su ne kabilan Yusuf ta wurin kabilansu.
38 The sons of Benjamin after their families: of Bela, the family of the Belaites; of Ashbel, the family of the Ashbelites; of Ahiram, the family of the Ahiramites;
Zuriyar Benyamin bisa ga kabilansu, daga Bela, kabilar Belawa; daga Ashbel, kabilar Ashbelawa; daga Ahiram, kabilar Ahiramawa;
39 of Shephupham, the family of the Shuphamites; of Hupham, the family of the Huphamites.
daga Shufam, kabilar Shufamawa; daga Hufam, kabilar Hufamawa.
40 The sons of Bela were Ard and Naaman: the family of the Ardites; and of Naaman, the family of the Naamites.
Zuriyar Bela daga Ard da Na’aman, daga Ard, kabilar Ardawa; daga Na’aman, kabilar Na’amawa;
41 These are the sons of Benjamin after their families; and those who were counted of them were forty-five thousand and six hundred.
Waɗannan su ne kabilan Benyamin, jimillarsu ta kai 45,600.
42 These are the sons of Dan after their families: of Shuham, the family of the Shuhamites. These are the families of Dan after their families.
Waɗannan su ne kabilan Dan bisa ga kabilarsu, daga Shuham, kabilar Shuhamawa. Waɗannan su ne kabilan Dan.
43 All the families of the Shuhamites, according to those who were counted of them, were sixty-four thousand and four hundred.
Dukansu kabilan Shuhamawa ne, jimillarsu ta kai 64,400.
44 The sons of Asher after their families: of Imnah, the family of the Imnites; of Ishvi, the family of the Ishvites; of Beriah, the family of the Berites.
Zuriyar Asher bisa ga kabilansu, daga Imna, kabilar Imnawa daga Ishbi, kabilar Ishbiyawa; daga Beriya, kabilar Beriyawa;
45 Of the sons of Beriah: of Heber, the family of the Heberites; of Malchiel, the family of the Malchielites.
daga zuriyar Beriya kuwa, daga Heber, kabilar Heberawa; daga Malkiyel, kabilar Malkiyelawa.
46 The name of the daughter of Asher was Serah.
(Asher yana da’ya mace da ake kira Sera.)
47 These are the families of the sons of Asher according to those who were counted of them, fifty-three thousand and four hundred.
Waɗannan su ne kabilan Asher; jimillarsu ta kai 53,400.
48 The sons of Naphtali after their families: of Jahzeel, the family of the Jahzeelites; of Guni, the family of the Gunites;
Zuriyar Naftali bisa ga kabilansu, daga Yazeyel, kabilar Yazeyelawa; daga Guni, kabilar Guniyawa;
49 of Jezer, the family of the Jezerites; of Shillem, the family of the Shillemites.
daga Yezer, kabilar Yezerawa; daga Shillem, kabilar Shillemawa.
50 These are the families of Naphtali according to their families; and those who were counted of them were forty-five thousand and four hundred.
Waɗannan su ne kabilan Naftali, jimillarsu ta kai 45,400.
51 These are those who were counted of the children of Israel, six hundred and one thousand and seven hundred and thirty.
Dukan jimillar mazan Isra’ila ta kai 601,730.
52 The LORD spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
53 “To these the land shall be divided for an inheritance according to the number of names.
“Ka rarraba musu ƙasar a matsayin gādo, bisa ga yawan kabila.
54 To the more you shall give the more inheritance, and to the fewer you shall give the less inheritance. To everyone according to those who were counted of him shall his inheritance be given.
Ga ƙungiya mafi girma, ka ba ta rabo mafi girma; ga ƙaramar ƙungiya kuwa, ka ba ta ƙarami rabo; kowane zai karɓa rabonsa ga yawan mutanen da aka rubuta.
55 Notwithstanding, the land shall be divided by lot. According to the names of the tribes of their fathers they shall inherit.
Ka tabbatar an rarraba ƙasar ta wurin rabo. Abin da kowace ƙungiya ta gāda zai zama bisa ga sunayen kabilar kakanninta.
56 According to the lot shall their inheritance be divided between the more and the fewer.”
Za a raba kowane gādo bisa ga rabo tsakanin manyan da ƙanana ƙungiyoyi.”
57 These are those who were counted of the Levites after their families: of Gershon, the family of the Gershonites; of Kohath, the family of the Kohathites; of Merari, the family of the Merarites.
Waɗannan su ne Lawiyawa da a ƙidaya bisa ga kabilansu, daga Gershom, kabilar Gershonawa; daga Kohat, kabilar Kohatawa; daga Merari, kabilar Merari.
58 These are the families of Levi: the family of the Libnites, the family of the Hebronites, the family of the Mahlites, the family of the Mushites, and the family of the Korahites. Kohath became the father of Amram.
Waɗannan kuma su ne kabilan Lawiyawa, kabilar Libniyawa, kabilar Hebronawa, kabilar Maliyawa, kabilar Mushiyawa, kabilar Korayawa (Kohat shi ne kakan Amram;
59 The name of Amram’s wife was Jochebed, the daughter of Levi, who was born to Levi in Egypt. She bore to Amram Aaron and Moses, and Miriam their sister.
sunan matan Amram shi ne Yokebed, ita zuriyar Lawi ce, wadda aka haifa wa Lawiyawa a Masar. A wajen Amram kuwa ta haifi Haruna, Musa da kuma’yar’uwarsu Miriyam.
60 To Aaron were born Nadab and Abihu, Eleazar and Ithamar.
Haruna shi ne mahaifin Nadab, Abihu, Eleyazar da kuma Itamar.
61 Nadab and Abihu died when they offered strange fire before the LORD.
Amma Nadab da Abihu sun mutu sa’ad da suka miƙa hadaya da haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji.)
62 Those who were counted of them were twenty-three thousand, every male from a month old and upward; for they were not counted amongst the children of Israel, because there was no inheritance given them amongst the children of Israel.
Dukan’ya’yan Lawiyawa maza daga wata ɗaya zuwa gaba, jimillarsu ta kai 23,000. Ba a ƙidaya su tare da sauran Isra’ilawa ba, domin ba a ba su gādo tare da su ba.
63 These are those who were counted by Moses and Eleazar the priest, who counted the children of Israel in the plains of Moab by the Jordan at Jericho.
Waɗannan su ne waɗanda Musa da Eleyazar firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a filaye Mowab kusa da Urdun a hayen Yeriko.
64 But amongst these there was not a man of them who were counted by Moses and Aaron the priest, who counted the children of Israel in the wilderness of Sinai.
Ba ko ɗayansu da yake cikin waɗanda Musa da Haruna firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a Hamadar Sinai.
65 For the LORD had said of them, “They shall surely die in the wilderness.” There was not a man left of them, except Caleb the son of Jephunneh, and Joshua the son of Nun.
Gama Ubangiji ya riga ya gaya wa waɗancan Isra’ilawa cewa lalle za su mutu a hamada, kuma ba ko ɗayansu da ya rage, sai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.

< Numbers 26 >