< Job 8 >

1 Then Bildad the Shuhite answered,
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 “How long will you speak these things? Shall the words of your mouth be a mighty wind?
“Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
3 Does God pervert justice? Or does the Almighty pervert righteousness?
Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
4 If your children have sinned against him, he has delivered them into the hand of their disobedience.
Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
5 If you want to seek God diligently, make your supplication to the Almighty.
Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
6 If you were pure and upright, surely now he would awaken for you, and make the habitation of your righteousness prosperous.
in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
7 Though your beginning was small, yet your latter end would greatly increase.
Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
8 “Please enquire of past generations. Find out about the learning of their fathers.
“Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
9 (For we are but of yesterday, and know nothing, because our days on earth are a shadow.)
gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
10 Shall they not teach you, tell you, and utter words out of their heart?
Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
11 “Can the papyrus grow up without mire? Can the rushes grow without water?
Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
12 While it is yet in its greenness, not cut down, it withers before any other reed.
Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
13 So are the paths of all who forget God. The hope of the godless man will perish,
Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
14 whose confidence will break apart, whose trust is a spider’s web.
Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
15 He will lean on his house, but it will not stand. He will cling to it, but it will not endure.
Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
16 He is green before the sun. His shoots go out along his garden.
Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
17 His roots are wrapped around the rock pile. He sees the place of stones.
shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
18 If he is destroyed from his place, then it will deny him, saying, ‘I have not seen you.’
Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
19 Behold, this is the joy of his way. Out of the earth, others will spring.
Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
20 “Behold, God will not cast away a blameless man, neither will he uphold the evildoers.
“Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
21 He will still fill your mouth with laughter, your lips with shouting.
Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
22 Those who hate you will be clothed with shame. The tent of the wicked will be no more.”
Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”

< Job 8 >