< Psalms 25 >

1 By David. To you, Yahweh, I lift up my soul.
Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
2 My God, I have trusted in you. Don’t let me be shamed. Don’t let my enemies triumph over me.
A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
3 Yes, no one who waits for you will be shamed. They will be shamed who deal treacherously without cause.
Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
4 Show me your ways, Yahweh. Teach me your paths.
Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
5 Guide me in your truth, and teach me, for you are the God of my salvation. I wait for you all day long.
ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
6 Yahweh, remember your tender mercies and your loving kindness, for they are from old times.
Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
7 Don’t remember the sins of my youth, nor my transgressions. Remember me according to your loving kindness, for your goodness’ sake, Yahweh.
Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
8 Good and upright is Yahweh, therefore he will instruct sinners in the way.
Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
9 He will guide the humble in justice. He will teach the humble his way.
Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
10 All the paths of Yahweh are loving kindness and truth to such as keep his covenant and his testimonies.
Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
11 For your name’s sake, Yahweh, pardon my iniquity, for it is great.
Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
12 What man is he who fears Yahweh? He shall instruct him in the way that he shall choose.
To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
13 His soul will dwell at ease. His offspring will inherit the land.
Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
14 The friendship of Yahweh is with those who fear him. He will show them his covenant.
Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
15 My eyes are ever on Yahweh, for he will pluck my feet out of the net.
Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
16 Turn to me, and have mercy on me, for I am desolate and afflicted.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
17 The troubles of my heart are enlarged. Oh bring me out of my distresses.
Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
18 Consider my affliction and my travail. Forgive all my sins.
Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
19 Consider my enemies, for they are many. They hate me with cruel hatred.
Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
20 Oh keep my soul, and deliver me. Let me not be disappointed, for I take refuge in you.
Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
21 Let integrity and uprightness preserve me, for I wait for you.
Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
22 God, redeem Israel out of all his troubles.
Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!

< Psalms 25 >