< Psalms 3 >

1 A Psalm by David, when he fled from Absalom his son. LORD, how my adversaries have increased! Many are those who rise up against me.
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
2 Many there are who say of my soul, “There is no help for him in God.” (Selah)
Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
3 But you, LORD, are a shield around me, my glory, and the one who lifts up my head.
Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
4 I cry to the LORD with my voice, and he answers me out of his holy hill. (Selah)
Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
5 I laid myself down and slept. I awakened, for the LORD sustains me.
Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
6 I will not be afraid of tens of thousands of people who have set themselves against me on every side.
Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
7 Arise, LORD! Save me, my God! For you have struck all of my enemies on the cheek bone. You have broken the teeth of the wicked.
Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
8 Salvation belongs to the LORD. May your blessing be on your people. (Selah)
Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)

< Psalms 3 >