< Lamentations 3 >
1 I am the man who has seen affliction by the rod of his wrath.
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 He has led me and caused me to walk in darkness, and not in light.
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 Surely he turns his hand against me again and again all day long.
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 He has made my flesh and my skin old. He has broken my bones.
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 He has built against me, and surrounded me with bitterness and hardship.
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 He has made me dwell in dark places, as those who have been long dead.
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 He has walled me about, so that I can’t go out. He has made my chain heavy.
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 Yes, when I cry, and call for help, he shuts out my prayer.
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 He has walled up my ways with cut stone. He has made my paths crooked.
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 He is to me as a bear lying in wait, as a lion in hiding.
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 He has turned away my path, and pulled me in pieces. He has made me desolate.
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 He has bent his bow, and set me as a mark for the arrow.
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 He has caused the shafts of his quiver to enter into my kidneys.
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 I have become a derision to all my people, and their song all day long.
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 He has filled me with bitterness. He has stuffed me with wormwood.
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 He has also broken my teeth with gravel. He has covered me with ashes.
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 You have removed my soul far away from peace. I forgot prosperity.
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 I said, “My strength has perished, along with my expectation from the LORD.”
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 Remember my affliction and my misery, the wormwood and the bitterness.
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 My soul still remembers them, and is bowed down within me.
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 This I recall to my mind; therefore I have hope.
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 It is because of the LORD’s loving kindnesses that we are not consumed, because his mercies don’t fail.
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 They are new every morning. Great is your faithfulness.
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 “The LORD is my portion,” says my soul. “Therefore I will hope in him.”
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 The LORD is good to those who wait for him, to the soul who seeks him.
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 It is good that a man should hope and quietly wait for the salvation of the LORD.
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 It is good for a man that he bear the yoke in his youth.
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 Let him sit alone and keep silence, because he has laid it on him.
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 Let him put his mouth in the dust, if it is so that there may be hope.
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 Let him give his cheek to him who strikes him. Let him be filled full of reproach.
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 For the Lord will not cast off forever.
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 For though he causes grief, yet he will have compassion according to the multitude of his loving kindnesses.
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 For he does not afflict willingly, nor grieve the children of men.
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 To crush under foot all the prisoners of the earth,
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 to turn away the right of a man before the face of the Most High,
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 to subvert a man in his cause, the Lord doesn’t approve.
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 Who is he who says, and it comes to pass, when the Lord doesn’t command it?
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 Doesn’t evil and good come out of the mouth of the Most High?
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 Why should a living man complain, a man for the punishment of his sins?
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 Let us search and try our ways, and turn again to the LORD.
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 Let’s lift up our heart with our hands to God in the heavens.
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 “We have transgressed and have rebelled. You have not pardoned.
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 “You have covered us with anger and pursued us. You have killed. You have not pitied.
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 You have covered yourself with a cloud, so that no prayer can pass through.
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 You have made us an off-scouring and refuse in the middle of the peoples.
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 “All our enemies have opened their mouth wide against us.
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 Terror and the pit have come on us, devastation and destruction.”
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 My eye runs down with streams of water, for the destruction of the daughter of my people.
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 My eye pours down and doesn’t cease, without any intermission,
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 until the LORD looks down, and sees from heaven.
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 My eye affects my soul, because of all the daughters of my city.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 They have chased me relentlessly like a bird, those who are my enemies without cause.
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 They have cut off my life in the dungeon, and have cast a stone on me.
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 Waters flowed over my head. I said, “I am cut off.”
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 I called on your name, LORD, out of the lowest dungeon.
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 You heard my voice: “Don’t hide your ear from my sighing, and my cry.”
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 You came near in the day that I called on you. You said, “Don’t be afraid.”
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 Lord, you have pleaded the causes of my soul. You have redeemed my life.
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 LORD, you have seen my wrong. Judge my cause.
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 You have seen all their vengeance and all their plans against me.
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 You have heard their reproach, LORD, and all their plans against me,
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 the lips of those that rose up against me, and their plots against me all day long.
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 You see their sitting down and their rising up. I am their song.
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 You will pay them back, LORD, according to the work of their hands.
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 You will give them hardness of heart, your curse to them.
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 You will pursue them in anger, and destroy them from under the heavens of the LORD.
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.