< John 7 >

1 After these things, Jesus was walking in Galilee, for he wouldn’t walk in Judea, because the Jews sought to kill him.
Bayan wannan, sai Yesu ya yi ta zagawa a cikin Galili, da ganga bai yarda yă je Yahudiya ba domin Yahudawa a can suna nema su kashe shi.
2 Now the feast of the Jews, the Feast of Booths, was at hand.
Amma sa’ad da Bikin Tabanakul na Yahudawa ya yi kusa,
3 His brothers therefore said to him, “Depart from here and go into Judea, that your disciples also may see your works which you do.
sai’yan’uwan Yesu suka ce masa, “Ya kamata ka bar nan ka tafi Yahudiya, don almajiranka su ga ayyukan banmamaki da kake yi.
4 For no one does anything in secret while he seeks to be known openly. If you do these things, reveal yourself to the world.”
Ba wanda yake so a san shi da zai yi abu a ɓoye. Da yake kana yin waɗannan abubuwa, sai ka nuna kanka ga duniya.”
5 For even his brothers didn’t believe in him.
Domin ko’yan’uwansa ma ba su gaskata da shi ba.
6 Jesus therefore said to them, “My time has not yet come, but your time is always ready.
Saboda haka Yesu ya ce musu, “Lokacina bai yi ba tukuna; amma a gare ku kowane lokaci daidai ne.
7 The world can’t hate you, but it hates me, because I testify about it, that its works are evil.
Duniya ba za tă iya ƙinku ba, amma ni take ƙi domin ina shaida cewa ayyukanta mugaye ne.
8 You go up to the feast. I am not yet going up to this feast, because my time is not yet fulfilled.”
Ku ku tafi Bikin, ba zan haura zuwa wannan Bikin ba yanzu, domin lokacina bai yi ba tukuna.”
9 Having said these things to them, he stayed in Galilee.
Da ya faɗa haka, sai ya dakata a Galili.
10 But when his brothers had gone up to the feast, then he also went up, not publicly, but as it were in secret.
Amma fa, bayan’yan’uwansa suka tafi Bikin, shi ma ya tafi, ba a fili ba, amma a ɓoye.
11 The Jews therefore sought him at the feast, and said, “Where is he?”
A Bikin kuwa, Yahudawa suka yi ta nemansa, suna cewa, “Ina mutumin yake?”
12 There was much murmuring among the multitudes concerning him. Some said, “He is a good man.” Others said, “Not so, but he leads the multitude astray.”
A cikin taron kuwa aka yi ta raɗe-raɗe game da shi. Waɗansu suka ce, “Shi mutumin kirki ne.” Waɗansu kuwa suka ce, “A’a, ai, ruɗin mutane yake.”
13 Yet no one spoke openly of him for fear of the Jews.
Amma ba wanda ya ce kome a fili game da shi don tsoron Yahudawa.
14 But when it was now the middle of the feast, Jesus went up into the temple and taught.
Sai bayan da aka kai tsakiyar Bikin, sa’an nan Yesu ya haura zuwa filin haikali ya fara koyarwa.
15 The Jews therefore marveled, saying, “How does this man know letters, having never been educated?”
Yahudawa suka yi mamaki suna tambaya, “Yaya wannan mutum ya sami wannan sani haka ba tare da ya yi wani karatu ba?”
16 Jesus therefore answered them, “My teaching is not mine, but his who sent me.
Yesu ya amsa ya ce, “Koyarwata ba tawa ba ce, ta fito ne daga wurin wanda ya aiko ni.
17 If anyone desires to do his will, he will know about the teaching, whether it is from God or if I am speaking from myself.
Duk wanda ya zaɓi yin nufin Allah, zai gane ko koyarwata daga Allah ce, ko kuwa don kaina ne nake magana.
18 He who speaks from himself seeks his own glory, but he who seeks the glory of him who sent him is true, and no unrighteousness is in him.
Mai magana don kansa, neman ɗaukakar kansa yake yi. Amma mai neman ɗaukakar wanda ya aiko shi, shi ne mai gaskiya, ba kuwa rashin gaskiya a gare shi.
19 Didn’t Moses give you the law, and yet none of you keeps the law? Why do you seek to kill me?”
Ashe, ba Musa ba ne ya ba ku Doka? Duk da haka ba ko ɗayanku da yake kiyaye Dokar. Me ya sa kuke nema ku kashe ni?”
20 The multitude answered, “You have a demon! Who seeks to kill you?”
Taron suka amsa suka ce, “Kana da aljani, wane ne yake so yă kashe ka?”
21 Jesus answered them, “I did one work and you all marvel because of it.
Yesu ya ce musu, “Na yi abin banmamaki ɗaya, dukanku kuwa kuka yi mamaki.
22 Moses has given you circumcision (not that it is of Moses, but of the fathers), and on the Sabbath you circumcise a boy.
Duk da haka, domin Musa ya bar muku kaciya (ko da yake a gaskiya, ba daga wurin Musa ne ya fito ba, sai dai daga wurin kakannin kakanninku), ga shi kuna yin wa yaro kaciya a ranar Asabbaci.
23 If a boy receives circumcision on the Sabbath, that the law of Moses may not be broken, are you angry with me because I made a man completely healthy on the Sabbath?
To, in za a iya yin wa yaro kaciya a ranar Asabbaci don kada a karya dokar Musa, don me kuke fushi da ni saboda na warkar da mutum a ranar Asabbaci?
24 Don’t judge according to appearance, but judge righteous judgment.”
Ku daina yin shari’a bisa ga ganin ido, sai dai ku yi shari’a bisa ga adalci.”
25 Therefore some of them of Jerusalem said, “Isn’t this he whom they seek to kill?
A nan ne fa waɗansu mutane daga Urushalima suka fara tambaya suna cewa, “Ashe, ba wannan mutum ne suke nema su kashe ba?
26 Behold, he speaks openly, and they say nothing to him. Can it be that the rulers indeed know that this is truly the Christ?
Ga shi nan yana magana a fili, su kuma ba su ce masa uffam ba. Ko hukumomi sun yarda cewa shi ne Kiristi?
27 However, we know where this man comes from, but when the Christ comes, no one will know where he comes from.”
Mun dai san inda mutumin nan ya fito; amma sa’ad da Kiristi ya zo ba wanda zai san inda ya fito.”
28 Jesus therefore cried out in the temple, teaching and saying, “You both know me, and know where I am from. I have not come of myself, but he who sent me is true, whom you don’t know.
Yesu yana cikin koyarwa a filin haikali ke nan, sai ya ɗaga murya ya ce, “I, kun san ni, kun kuma san inda na fito. Ban zo don kaina ba, sai dai shi da ya aiko ni mai gaskiya ne. Ba ku san shi ba,
29 I know him, because I am from him, and he sent me.”
amma na san shi, domin ni daga wurinsa ne, kuma shi ya aiko ni.”
30 They sought therefore to take him; but no one laid a hand on him, because his hour had not yet come.
Da jin haka, sai suka yi ƙoƙari su kama shi, sai dai ba wanda ya taɓa shi, don lokacinsa bai yi ba tukuna.
31 But of the multitude, many believed in him. They said, “When the Christ comes, he won’t do more signs than those which this man has done, will he?”
Duk da haka, da yawa a cikin taron suka ba da gaskiya gare shi. Suka ce, “Sa’ad da Kiristi ya zo, zai yi abubuwan banmamaki fiye da na wannan mutum ne?”
32 The Pharisees heard the multitude murmuring these things concerning him, and the chief priests and the Pharisees sent officers to arrest him.
Farisiyawa suka ji taron suna raɗe-raɗen waɗannan abubuwa game da shi. Sai manyan firistoci da Farisiyawa suka aiki masu gadin haikalin su kama shi.
33 Then Jesus said, “I will be with you a little while longer, then I go to him who sent me.
Sai Yesu ya ce, “Ina tare da ku na ɗan ƙanƙanin lokaci ne kawai, sa’an nan zan koma wurin wanda ya aiko ni.
34 You will seek me and won’t find me. You can’t come where I am.”
Za ku neme ni, amma ba za ku same ni ba; inda nake kuwa, ba za ku iya zuwa ba.”
35 The Jews therefore said among themselves, “Where will this man go that we won’t find him? Will he go to the Dispersion among the Greeks and teach the Greeks?
Sai Yahudawa suka ce wa juna, “Ina mutumin nan yake niyyar tafiya da ba za mu iya samunsa ba? Zai je wurin mutanenmu da suke zaune warwatse a cikin Hellenawa, yă kuma koya wa Hellenawa ne?
36 What is this word that he said, ‘You will seek me, and won’t find me;’ and ‘Where I am, you can’t come’?”
Me yake nufi da ya ce, ‘Za ku neme ni, amma ba za ku same ni ba,’ da kuma ‘Inda nake, ba za ku iya zuwa ba’?”
37 Now on the last and greatest day of the feast, Jesus stood and cried out, “If anyone is thirsty, let him come to me and drink!
A rana ta ƙarshe kuma mafi girma ta Bikin, Yesu ya tsaya ya yi magana da babbar murya ya ce, “Duk mai jin ƙishirwa, yă zo wurina yă sha.
38 He who believes in me, as the Scripture has said, from within him will flow rivers of living water.”
Duk wanda ya gaskata da ni, kamar yadda Nassi ya ce, kogunan ruwa masu rai za su gudana daga cikinsa.”
39 But he said this about the Spirit, which those believing in him were to receive. For the Holy Spirit was not yet given, because Jesus wasn’t yet glorified.
Da wannan yana nufin Ruhu ke nan, wanda waɗanda suka gaskata da shi za su karɓa daga baya. Har yă zuwa wannan lokaci ba a ba da Ruhu ba tukuna, da yake ba a riga an ɗaukaka Yesu ba.
40 Many of the multitude therefore, when they heard these words, said, “This is truly the prophet.”
Da jin kalmominsa, waɗansu mutane suka ce, “Ba shakka, mutumin nan shi ne Annabin.”
41 Others said, “This is the Christ.” But some said, “What, does the Christ come out of Galilee?
Waɗansu suka ce, “Shi ne Kiristi.” Waɗansu har wa yau suka ce, “Yaya Kiristi zai fito daga Galili?
42 Hasn’t the Scripture said that the Christ comes of the offspring of David, and from Bethlehem, the village where David was?”
Nassi bai ce Kiristi zai fito daga zuriyar Dawuda, daga kuma Betlehem garin da Dawuda ya zauna ba?”
43 So a division arose in the multitude because of him.
Sai mutanen suka rabu saboda Yesu.
44 Some of them would have arrested him, but no one laid hands on him.
Waɗansu suka so su kama shi, sai dai ba wanda ya taɓa shi.
45 The officers therefore came to the chief priests and Pharisees; and they said to them, “Why didn’t you bring him?”
A ƙarshe masu gadin haikali suka koma wurin manyan firistocin da Farisiyawa, waɗanda suka tambaye su cewa, “Don me ba ku kawo shi nan ba?”
46 The officers answered, “No man ever spoke like this man!”
Sai masu gadin suka ce, “Kai, babu wanda ya taɓa magana kamar wannan mutum.”
47 The Pharisees therefore answered them, “You aren’t also led astray, are you?
Sai Farisiyawa suka amsa cikin fushi suka ce, “Af, kuna nufi har da ku ma ya ruɗe ku ke nan?
48 Have any of the rulers or any of the Pharisees believed in him?
Akwai wani daga cikin masu mulki ko cikin Farisiyawan da ya gaskata da shi?
49 But this multitude that doesn’t know the law is cursed.”
A’a! Sai dai wannan taron da ba su san kome game da Doka ba, la’anannu ne.”
50 Nicodemus (he who came to him by night, being one of them) said to them,
Nikodimus, wanda ya je wurin Yesu dā, wanda kuma yake ɗayansu ya ce,
51 “Does our law judge a man unless it first hears from him personally and knows what he does?”
“Ashe, dokarmu takan hukunta mutum ba tare da an fara ji daga bakinsa game da abin da yake yi ba?”
52 They answered him, “Are you also from Galilee? Search and see that no prophet has arisen out of Galilee.”
Sai suka amsa suka ce, “Kai ma daga Galili ne? Bincika ka gani, za ka iske cewa ba annabin da zai fito daga Galili.”
53 Everyone went to his own house,
Sai kowannensu ya koma gidansa.

< John 7 >