< 1 Timothy 2 >

1 I exhort therefore, first of all, that petitions, prayers, intercessions, and givings of thanks be made for all men,
Da farko dai, ina gargaɗe ku cewa a yi roƙe-roƙe, ana addu’o’i, ana yin addu’a a madadin waɗansu da kuma a yi godiya saboda kowane mutum
2 for kings and all who are in high places, that we may lead a tranquil and quiet life in all godliness and reverence.
da sarakuna da dukan masu mulki, domin mu zauna lafiya, rai kuma kwance, muna bin Allah sosai a cikin natsuwa.
3 For this is good and acceptable in the sight of God our Savior,
Wannan yana da kyau, yakan kuma gamshi Allah Mai Cetonmu,
4 who desires all people to be saved and come to full knowledge of the truth.
wanda yake so dukan mutane su sami ceto su kuma zo ga sanin gaskiya.
5 For there is one God and one mediator between God and men, the man Christ Jesus,
Gama Allah ɗaya ne, matsakanci kuma ɗaya tsakanin Allah da mutane, shi ne kuwa Kiristi Yesu,
6 who gave himself as a ransom for all, the testimony at the proper time,
wanda ya ba da kansa fansa domin dukan mutane, shaidar da aka bayar a daidai lokaci.
7 to which I was appointed a preacher and an apostle—I am telling the truth in Christ, not lying—a teacher of the Gentiles in faith and truth.
Don haka ne aka sa ni mai wa’azi, da manzo kuma, gaskiya nake faɗa, ba ƙarya ba, na kuma zama malami mai koya wa al’ummai al’amarin bangaskiya da kuma na gaskiya.
8 I desire therefore that the men in every place pray, lifting up holy hands without anger and doubting.
Ina so maza a ko’ina su ɗaga hannuwansu masu tsarki cikin addu’a, ba tare da fushi ko faɗa ba.
9 In the same way, that women also adorn themselves in decent clothing, with modesty and propriety, not with braided hair, gold, pearls, or expensive clothing,
Ina kuma so mata su lura su yi wa kansu adon da ya cancanta, da rigunan da suka dace, ba da adon kitso ko sa kayan zinariya ko lu’ulu’u ko kuma tufafi masu tsada ba,
10 but with good works, which is appropriate for women professing godliness.
sai dai su yi ayyuka masu kyan da suka dace da matan da suke masu bauta wa Allah.
11 Let a woman learn in quietness with full submission.
Ya kamata mace ta riƙa koyo cikin natsuwa da cikakkiyar biyayya.
12 But I don’t permit a woman to teach, nor to exercise authority over a man, but to be in quietness.
Ban ba mace izini ta koyar ko tă yi mulki a kan namiji ba; sai dai ta zauna shiru.
13 For Adam was formed first, then Eve.
Gama Adamu ne aka fara halitta, sa’an nan Hawwa’u.
14 Adam wasn’t deceived, but the woman, being deceived, has fallen into disobedience;
Ba kuma Adamu ne aka yaudara ba; macen ce aka yaudara ta kuma zama mai zunubi.
15 but she will be saved through her childbearing, if they continue in faith, love, and holiness with sobriety.
Amma mata Za tă sami ceto za su sami ceto ta wurin haihuwa, in suka ci gaba cikin bangaskiya, ƙauna da kuma tsarki tare da halin sanin ya kamata.

< 1 Timothy 2 >