< Matthew 28 >
1 Now after the Sabbath, as it began to dawn on the first day of the week, Mary Magdalene and the other Mary came to see the tomb.
Da daddare ranar Asabaci, rana ta fari ga mako ta fara gabatowa, Maryamu Magadaliya da daya Maryamun suka zo don su ziyarci kabarin.
2 Behold, there was a great earthquake, for an angel of the Lord descended from the sky and came and rolled away the stone from the door and sat on it.
Sai aka yi girgizar kasa mai karfi, saboda mala'ikan Ubangiji ya sauko daga sama ya kuma murgine dutsen ya zauna a kai.
3 His appearance was like lightning, and his clothing white as snow.
Kamanninsa kamar walkiya, tufafinsa kuma fari fat kamar suno.
4 For fear of him, the guards shook, and became like dead men.
Masu tsaron suka razana don tsoro suka zama kamar matattun mutane.
5 The angel answered the women, “Don’t be afraid, for I know that you seek Jesus, who has been crucified.
Mala'ikan ya yi wa matan magana cewa, “Kada ku ji tsoro, nasan kuna neman Yesu wanda aka gicciye.
6 He is not here, for he has risen, just like he said. Come, see the place where the Lord was lying.
Baya nan, amma ya tashi kamar yadda ya fada. Ku zo ku ga wurin da aka kwantar da shi.
7 Go quickly and tell his disciples, ‘He has risen from the dead, and behold, he goes before you into Galilee; there you will see him.’ Behold, I have told you.”
Ku hanzarta ku gaya wa almajiransa, 'Ya tashi daga matattu. Duba, ya tafi Galili, can zaku same shi.' Gashi ni kuwa na fada maku.”
8 They departed quickly from the tomb with fear and great joy, and ran to bring his disciples word.
Matan suka yi hanzari suka bar kabarin da tsoro da murna, suka ruga domin su sanar wa almajiransa.
9 As they went to tell his disciples, behold, Jesus met them, saying, “Rejoice!” They came and took hold of his feet, and worshipped him.
Sai ga Yesu ya tare su, yace masu, “A gaishe ku.” Sai matan suka kama kafar sa, suka kuma yi masa sujada.
10 Then Jesus said to them, “Don’t be afraid. Go tell my brothers that they should go into Galilee, and there they will see me.”
Sai Yesu yace masu, “Kada ku ji tsoro. Ku je ku fada wa 'yan'uwana su je Galili. Can zasu ganni.”
11 Now while they were going, behold, some of the guards came into the city and told the chief priests all the things that had happened.
Sa'adda matan suke tafiya, sai wadansu masu tsaro suka shiga gari suka fada wa Shugabanin Firistoci dukan abin da ya faru.
12 When they were assembled with the elders and had taken counsel, they gave a large amount of silver to the soldiers,
Firistocin suka hadu da dattawa suka tattauna al'amarin, sai suka bada kudi masu yawa ga sojojin
13 saying, “Say that his disciples came by night and stole him away while we slept.
Sukace masu, “Ku gaya wa sauran cewa, “Almajiran Yesu sun zo da daddare sun sace gangar jikinsa lokacin da muke barci.”
14 If this comes to the governor’s ears, we will persuade him and make you free of worry.”
Idan wannan rahoto ya isa wurin gwamna, za mu lallashe shi mu ja hankalinsa mu raba ku da damuwa.”
15 So they took the money and did as they were told. This saying was spread abroad amongst the Jews, and continues until today.
Sai sojojin suka karbi kudin suka yi abinda aka umarcesu. Wannan rahoto ya bazu a tsakanin Yahudawa, ya ci gaba har zuwa yau.
16 But the eleven disciples went into Galilee, to the mountain where Jesus had sent them.
Amma almajiran sha daya suka tafi Galili, kan dutsen da Yesu ya umarcesu.
17 When they saw him, they bowed down to him; but some doubted.
Da suka gan shi, suka yi masa sujada, amma wadansu suka yi shakka.
18 Jesus came to them and spoke to them, saying, “All authority has been given to me in heaven and on earth.
Yesu ya zo wurin su ya yi masu magana, yace, “Dukan iko dake sama da kasa an ba ni.
19 Go and make disciples of all nations, baptising them in the name of the Father and of the Son and of the Holy Spirit,
Sai kuje ku almajirantar da dukan al'ummai. Kuna yi masu baftisma cikin sunan Uba da na Da da na Ruhu Mai Tsarki.
20 teaching them to observe all things that I commanded you. Behold, I am with you always, even to the end of the age.” Amen. (aiōn )
Ku koya masu su kiyaye dukan abin da na umarce ku. Duba, ni kuma kullum ina tare da ku har karshen zamani.” (aiōn )