< Revelation 6 >

1 And when the Lamb broke one of the seven seals I saw it, and I heard one of the four living creatures say, as if in a voice of thunder, "Come."
Na kalli yayinda Ɗan Ragon ya buɗe hatimin farko na hatimai bakwai ɗin nan. Sai na ji ɗaya daga cikin halittu huɗun nan masu rai ya yi magana da murya mai kama da tsawa ya ce, “Zo!”
2 And I looked and a white horse appeared, and its rider carried a bow; and a victor's wreath was given to him; and he went out conquering and in order to conquer.
Na duba, can kuwa a gabana ga wani farin doki! Mai hawansa yana riƙe da baka, aka kuma ba shi rawani, ya yi sukuwa ya fito kamar mai nasara da ya kutsa don nasara.
3 And when the Lamb broke the second seal, I heard the second living creature say, "Come."
Sa’ad da Ɗan Ragon ya buɗe hatimi na biyun, sai na ji halitta mai rai na biyu ya ce, “Zo!”
4 And another horse came out--a fiery-red one; and power was given to its rider to take peace from the earth, and to cause men to kill one another; and a great sword was given to him.
Sai wani doki ya fito, ja wur. Aka ba wa mai hawansa iko yă ɗauke salama daga duniya yă kuma sa mutane su kashe juna. Aka ba shi babban takobi.
5 When the Lamb broke the third seal, I heard the third living creature say, "Come." I looked, and a black horse appeared, its rider carrying a balance in his hand.
Sa’ad da Ɗan Ragon ya buɗe hatimi na uku, sai na ji halitta mai rai na uku ya ce, “Zo!” Na duba, can a gabana kuwa ga wani baƙin doki! Mai hawansa yana riƙe da abubuwan awo guda biyu a hannunsa.
6 And I heard what seemed to be a voice speaking in the midst of the four living creatures, and saying, "A quart of wheat for a shilling, and three quarts of barley for a shilling; but do not injure either the oil or the wine."
Sai na ji wani abu mai ƙara kamar wata murya a tsakiyar halittu huɗun nan masu rai tana cewa, “Kwatan alkama don albashin aikin yini, da kuma kwata uku na sha’ir don albashin yini guda, kada kuwa ka ɓata man da ruwan inabi!”
7 When the Lamb broke the fourth seal I heard the voice of the fourth living creature say, "Come."
Sa’ad da Ɗan Ragon ya buɗe hatimi na huɗu, sai na ji muryar halitta mai rai na huɗu ya ce, “Zo!”
8 I looked and a pale-colored horse appeared. Its rider's name was Death, and Hades came close behind him; and authority was given to them over the fourth part of the earth, to kill with the sword or with famine or pestilence or by means of the wild beasts of the earth. (Hadēs g86)
Na duba, can a gabana kuwa ga ƙodaɗɗen doki! An ba wa mai hawansa suna Mutuwa, Hades kuwa yana biye da shi. Aka ba su iko a kan kashi ɗaya bisa huɗu na duniya don su yi kisa da takobi, yunwa da annoba, har ma da namomin jeji na duniya. (Hadēs g86)
9 When the Lamb broke the fifth seal, I saw at the foot of the altar the souls of those whose lives had been sacrificed because of the word of God and of the testimony which they had given.
Sa’ad da ya buɗe hatimi na biyar, sai na ga a ƙarƙashin bagaden rayukan waɗanda aka kashe saboda maganar Allah da kuma shaidar da suka yi.
10 And now in loud voices they cried out, saying, "How long, O Sovereign Lord, the holy One and the true, dost Thou delay judgment and the taking of vengeance upon the inhabitants of the earth for our blood?"
Suka yi kira da babbar murya suka ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, Mai Tsarki da kuma Mai Gaskiya, sai yaushe za ka shari’anta mazaunan duniya ka kuma ɗauki mana fansar jininmu?”
11 And there was given to each of them a long white robe, and they were bidden to wait patiently for a short time longer, until the full number of their fellow bondservants should also complete--namely of their brethren who were soon to be killed just as they had been.
Sai aka ba wa kowannensu farin riga, aka kuma faɗa musu su ɗan jira kaɗan sai an cika adadin abokansu masu hidima da kuma’yan’uwansu waɗanda za a kashe kamar yadda su ma aka kashe su.
12 When the Lamb broke the sixth seal I looked, and there was a great earthquake, and the sun became as dark as sackcloth, and the whole disc of the moon became like blood.
Ina kallo yayinda ya buɗe hatimi na shida. Sai aka yi babban girgizar ƙasa. Rana ta zama baƙa kamar gwado na gashin akuya, wata kuma gaba ɗaya ya zama ja wur kamar jini,
13 The stars in the sky also fell to the earth, as when a fig-tree, upon being shaken by a gale of wind, casts its unripe figs to the ground.
taurarin sararin sama suka fāffāɗi a ƙasa, kamar yadda ɗanyun’ya’yan ɓaure suke fāɗuwa daga itacen ɓaure sa’ad da iska mai ƙarfi ta jijjiga shi.
14 The sky too passed away, as if a scroll were being rolled up, and every mountain and island was removed from its place.
Sararin sama kuwa ya janye kamar naɗaɗɗen littafi, ya yi ta naɗewa, aka kuma kawar da kowane dutse da kowane tsibiri daga wurinsa.
15 The kings of the earth and the great men, the military chiefs, the wealthy and the powerful--all, whether slaves or free men--hid themselves in the caves and in the rocks of the mountains,
Sa’an nan sarakunan duniya, hakimai, jarumawa, masu arziki, masu ƙarfi, da kowane bawa da kuma kowane’yantacce ya ɓoye a cikin koguna da kuma cikin duwatsun tsaunuka.
16 while they called to the mountains and the rocks, saying, "Fall on us and hide us from the presence of Him who sits on the throne and from the anger of the Lamb;
Suka kira duwatsu da tsaunuka suna cewa, “Ku fāɗi a kanmu ku kuma ɓoye mu daga fuskar wannan mai zama a kan kursiyi da kuma daga fushin Ɗan Ragon nan!
17 for the day of His anger--that great day--has come, and who is able to stand?"
Gama babbar ranar fushinsu ta zo, wa kuwa zai iya tsayawa?”

< Revelation 6 >