< Revelation 1 >

1 The revelation given by Jesus Christ, which God granted Him, that He might make known to His servants certain events which must shortly come to pass: and He sent His angel and communicated it to His servant John.
Wannan shine wahayin Yesu Almasihu da Allah ya bashi ya nuna wa bayinsa abinda zai faru ba da dadewa ba. Ya bayyana wannan ta wurin aiko da mala'ikansa ga bawansa Yahaya.
2 This is the John who taught the truth concerning the Word of God and the truth told us by Jesus Christ-- a faithful account of what he had seen.
Yahaya yayi shaida akan abinda ya gani game da maganar Allah da kuma shaidar da aka bayar game da Yesu Almasihu.
3 Blessed is he who reads and blessed are those who listen to the words of this prophecy and lay to heart what is written in it; for the time for its fulfillment is now close at hand.
Mai albarka ne wanda ke karanta littafin nan da murya mai karfi, da kuma wadanda ke sauraron kalmomin wannan annabci kuma suke biyayya da abinda aka rubuta a ciki, domin kuwa lokaci ya kusato.
4 John sends greetings to the seven Churches in the province of Asia. May grace be granted to you, and peace, from Him who is and was and evermore will be; and from the seven Spirits which are before His throne;
Ni Yahaya, zuwa ga ikilisiyoyi bakwai na kasar Asiya: alheri zuwa gare ku da salama daga wanda ke yanzu, wanda ya kuma kasance a da, shi ne kuma mai zuwa nan gaba, kuma daga ruhohin nan bakwai da ke gaban kursiyinsa,
5 and from Jesus Christ, the truthful witness, the first of the dead to be born to Life, and the Ruler of the kings of the earth. To Him who loves us and has freed us from our sins with His own blood,
kuma daga Yesu Almasihu, wanda ke amintaccen mashaidi, dan fari na tashi daga cikin matattu, kuma mai mulkin sarakunan duniya. Ga wanda ya ke kaunar mu ya kuma kwance mu daga daurin zunubanmu ta wurin jininsa,
6 and has formed us into a Kingdom, to be priests to God, His Father--to Him be ascribed the glory and the power until the Ages of the Ages. Amen. (aiōn g165)
ya maishe mu masu mulki, firistoci na Allahnsa da Ubansa - daukaka da iko su tabbata gare shi har abada abadin, Amin. (aiōn g165)
7 He is coming in the clouds, and every eye will see Him, and so will those who pierced Him; and all the nations of the earth will gaze on Him and mourn. Even so. Amen.
Duba yana zuwa tare da gizagizai, kowane ido zai gan shi, har ma da wadanda suka soke shi. Haka kuma dukkan kabilun duniya za su yi makoki saboda da shi. I, Amin.
8 "I am the Alpha and the Omega," says the Lord God, "He who is and was and evermore will be--the Ruler of all."
“Nine na farko da na karshe”, in ji Ubangiji Allah, “Wanda yake shine a yanzu, shine wanda ya kasance a da, kuma shi ne mai zuwa nan gaba, Mai iko duka.”
9 I John, your brother, and a sharer with you in the sorrows and Kingship and patient endurance of Jesus, found myself in the island of Patmos, on account of the Word of God and the truth told us by Jesus.
Ni, Yahaya- dan'uwan ku da wanda ke tarayya daku cikin shan wahala, da mulki da tsawon jimrewa wadanda ke cikin Yesu - ina tsibirin da ake kira Batmusa saboda maganar Allah da kuma shaida game da Yesu.
10 In the Spirit I found myself present on the day of the Lord, and I heard behind me a loud voice which resembled the blast of a trumpet.
Ina cikin Ruhu a ranar Ubangiji. Sai naji wata murya mai karfi a baya na kamar ta kaho.
11 It said, "Write forthwith in a roll an account of what you see, and send it to the seven Churches--to Ephesus, Smyrna, Pergamum, Thyateira, Sardis, Philadelphia and Laodicea."
Ta ce, “Rubuta abinda ka gani a cikin littafi, ka kuma aika wa ikilisiyoyin nan bakwai - ga Afisus, ga Simirna, ga Birgamas, ga Tayatira, ga Sardisu, ga Filadalfiya, da kuma ga Laudikiya.”
12 I turned to see who it was that was speaking to me; and then I saw seven golden lampstands,
Na juya don in ga wanda muryarsa ke magana da ni, da na juya sai na ga fitilu bakwai akan madorin su
13 and in the center of the lampstands some One resembling the Son of Man, clothed in a robe which reached to His feet, and with a girdle of gold across His breast.
A tsakiyar fitilun akwai wani mai kama da dan mutum, yana sanye da doguwar tufa har tafin sawunsa, da damara ta zinariya kewaye a kirjinsa.
14 His head and His hair were white, like white wool--as white as snow; and His eyes resembled a flame of fire.
Kansa da gashinsa fari fat kamar auduga - kamar dusar kankara, kuma idanun sa kamar harshen wuta.
15 His feet were like silver-bronze, when it is white-hot in a furnace; and His voice resembled the sound of many waters.
Kafaffunsa kamar gogaggiyar tagulla, kamar tagullar da aka tace da wutar makera, muryar sa kuma kamar kugin ambaliyar ruwan teku ne.
16 In His right hand He held seven stars, and a sharp, two-edged sword was seen coming from His mouth; and His glance resembled the sun when it is shining with its full strength.
A hannunsa na dama yana rike da taurari bakwai, daga bakinsa kuma kakkaifan takobi mai kaifi biyu ke fitowa. Fuskarsa tana haskakawa kamar sa'adda rana ke haskakawa kwarai.
17 When I saw Him, I fell at His feet as if I were dead. But He laid His right hand upon me and said, "Do not be afraid: I am the First and the Last, and the ever-living One.
Lokacin da na gan shi, na fadi kamar mataccen mutum a kafaffunsa. Ya dora hannunsa na dama a kaina ya ce, “Kada ka ji tsoro. Nine na farko da na karshe,
18 I died; but I am now alive until the Ages of the Ages, and I have the keys of the gates of Death and of Hades! (aiōn g165, Hadēs g86)
da kuma wanda ke raye. Na mutu, amma duba ina raye har abada! Kuma ina da mabudin mutuwa da na hades. (aiōn g165, Hadēs g86)
19 Write down therefore the things you have just seen, and those which are now taking place, and those which are soon to follow:
Domin haka ka rubuta abinda ka gani, abin da ke yanzu, da abin da zai faru bayan wanan.
20 the secret meaning of the seven stars which you have seen in My right hand, and of the seven lampstands of gold. The seven stars are the ministers of the seven Churches, and the seven lampstands are the seven Churches.
Akan boyayyar ma'ana game da taurari bakwai da ka gani a hannun dama na, da madorin fitilu bakwai na zinariya: Taurarin nan bakwai mala'iku ne na ikilisiyoyi bakwai, kuma madorin fitilun nan bakwai ikilisiyoyi ne bakwai.

< Revelation 1 >