< Mark 11 >
1 When they were getting near Jerusalem and had arrived at Bethphage and Bethany, on the Mount of Olives, Jesus sent two of his disciples on in front, with these instructions.
Sa’ad da suka yi kusa da Urushalima, suka zo Betfaji da Betani wajen Dutsen Zaitun, sai Yesu ya aiki biyu daga cikin almajiransa,
2 "Go," He said, "to the village facing you, and immediately on entering it you will find an ass's foal tied up which no one has ever yet ridden: untie him and bring him here.
ya ce musu, “Ku je ƙauyen da yake gaba da ku, da shigarku, za ku tarar da wani ɗan jaki a daure a can, wanda ba wanda ya taɓa hawa. Ku kunce shi ku kawo nan.
3 And if any one asks you, 'Why are you doing that?' say, 'The Master needs it, and will send it back here without delay.'"
In wani ya tambaye ku, ‘Don me kuke yin haka?’ Ku gaya masa cewa, ‘Ubangiji yana bukatarsa, zai kuma dawo da shi ba da jimawa ba.’”
4 So they went and found a young ass tied up at the front door of a house. They were untying it,
Suka tafi, suka kuwa tarar da wani ɗan jaki a waje, a titi, daure a ƙofar gida. Suna cikin kunce shi ke nan,
5 when some of the bystanders called out, "What are you doing, untying the foal?"
sai waɗansu mutane da suke tsattsaye a wurin suka ce musu, “Me kuke yi da kuke kunce ɗan jakin nan?”
6 But on their giving the answer that Jesus had bidden them give, they let them take it.
Suka amsa kamar yadda Yesu ya ce su yi. Mutanen kuwa suka ƙyale su.
7 So they brought the foal to Jesus, and threw their outer garments over him; and Jesus mounted.
Da suka kawo shi wajen Yesu, sai suka shimfiɗa rigunarsu a bayansa. Yesu kuwa ya hau ya zauna bisansa.
8 Then many spread their outer garments to carpet the road, and others leafy branches which they had cut down in the fields;
Mutane da yawa suka shimfiɗa rigunarsu a kan hanya, waɗansu kuma suka baza rassan itatuwan da suka sara daga gonaki.
9 while those who led the way and those who followed kept shouting "God save Him!" Blessed be He who comes in the Lord's name.
Waɗanda suka yi gaba, da kuma waɗanda suke biye, duk suka ɗaga murya, suna cewa, “Hosanna!” “Mai albarka ne wanda yake zuwa a cikin sunan Ubangiji!”
10 Blessings on the coming Kingdom of our forefather David! God in the highest Heavens save Him!"
“Mai albarka ne mulkin nan mai zuwa na mahaifinmu Dawuda!” “Hosanna a can cikin samaniya!”
11 So He came into Jerusalem and into the Temple; and after looking round upon everything there, the hour being now late He went out to Bethany with the Twelve.
Yesu ya shiga Urushalima ya kuma tafi filin haikali. Ya dudduba kome duka, amma da yake yamma ta yi, sai ya tafi Betani tare da Sha Biyun.
12 The next day, after they had left Bethany, He was hungry.
Kashegari, da suke barin Betani, Yesu kuwa ya ji yunwa.
13 But in the distance He saw a fig-tree in full leaf, and went to see whether perhaps He could find some figs on it. When however He came to it, He found nothing but leaves (for it was not fig time);
Da ya hangi wani itacen ɓaure mai ganye, sai ya je domin yă ga ko yana da’ya’ya. Amma da ya kai can, bai tarar da kome ba sai ganye, domin ba lokacin’ya’yan ɓaure ba ne.
14 and He said to the tree, "Let no one ever again eat fruit from thee!" And His disciples heard this. (aiōn )
Sai ya ce wa itacen, “Kada kowa yă ƙara cin’ya’yanka.” Almajiransa kuwa suka ji ya faɗi haka. (aiōn )
15 They reached Jerusalem, and entering the Temple He began to drive out the buyers and sellers, and upset the money-changers' tables and the stools of the pigeon-dealers,
Da suka kai Urushalima, sai Yesu ya shiga filin haikalin, ya fara korar waɗanda suke saya da sayarwa a can. Ya tutture tebur na masu musayar kuɗi, da kujerun masu sayar da tattabaru,
16 and would not allow any one to carry anything through the Temple.
ya kuma hana kowa yă ratsa da a filin haikali ɗauke da kayan ciniki.
17 And He remonstrated with them. "Is it not written," He said, "'My House shall be called The House of Prayer for all the nations?' But you have made it what it now is--a robbers' cave."
Da yake koya musu, sai ya ce, “Ashe, ba a rubuce yake ba cewa, ‘Za a kira gidana, gidan addu’a na dukan al’ummai ba’? Amma ga shi kun mai da shi ‘kogon’yan fashi.’”
18 This the High Priests and Scribes heard, and they began to devise means to destroy Him. For they were afraid of Him, because of the deep impression produced on all the people by His teaching.
Manyan firistoci da malaman dokoki suka ji wannan, sai suka fara neman hanyar da za su kashe shi, gama suna jin tsoronsa, saboda dukan taron suna mamakin koyarwarsa.
19 When evening came on, Jesus and His disciples used to leave the city.
Da yamma ta yi, sai Yesu da almajiransa suka bar garin.
20 In the early morning, as they passed by, they saw the fig-tree withered to the roots;
Da safe, da suke wucewa, sai suka ga itacen ɓauren nan ya yanƙwane tun daga saiwarsa.
21 and Peter, recollecting, said to Him, "Look, Rabbi, the fig-tree which you cursed is withered up."
Bitrus ya tuna, sai ya ce wa Yesu, “Rabbi, duba! Itacen ɓauren nan da ka la’anta, ya yanƙwane!”
22 Jesus said to them, "Have faith in God.
Yesu ya amsa ya ce, “Ku gaskata da Allah.
23 In solemn truth I tell you that if any one shall say to this mountain, 'Remove, and hurl thyself into the sea,' and has no doubt about it in his heart, but stedfastly believes that what he says will happen, it shall be granted him.
Gaskiya nake gaya muku, in wani ya ce wa dutsen nan, ‘Je ka, ka fāɗa cikin teku,’ bai kuwa yi shakka a zuciyarsa ba, amma ya gaskata cewa, abin da ya faɗa zai faru, haka kuwa za a yi masa.
24 That is why I tell you, as to whatever you pray and make request for, if you believe that you have received it it shall be yours.
Saboda haka, ina faɗa muku, duk abin da kuka roƙa cikin addu’a, ku gaskata kun riga kun karɓa, zai kuwa zama naku.
25 But whenever you stand praying, if you have a grievance against any one, forgive it, so that your Father in Heaven may also forgive you your offences."
A duk lokacin da kuke tsaye cikin addu’a, in kuna riƙe da wani mutum a zuciyarku, ku gafarta masa, domin Ubanku da yake sama shi ma yă gafarta muku zunubanku.”
27 They came again to Jerusalem; and as He was walking in the Temple, the High Priests, Scribes and Elders came to Him
Suka sāke dawowa cikin Urushalima. Da Yesu yana tafiya a filin haikali, sai manyan firistoci, malaman dokoki da kuma dattawa suka zo wurinsa.
28 and asked, "By what authority are you doing these things? and who gave you authority to do them?"
Suka tambaye, shi suka ce, “Da wane iko kake yin waɗannan abubuwa? Wa kuma ya ba ka ikon yin wannan?”
29 "And I will put a question to you," replied Jesus; "answer me, and then I will tell you by what authority I do these things.
Yesu ya ce, “Zan yi muku tambaya guda. Ku ba ni amsa, ni kuma zan gaya muku, ko da wane iko nake yin waɗannan abubuwa.
30 John's Baptism--was it of Heavenly or of human origin? Answer me."
Baftismar Yohanna, daga sama ce, ko daga mutane? Ku faɗa mini!”
31 So they debated the matter with one another. "Suppose we say, 'Heavenly,'" they argued, "he will ask, 'Why then did you not believe him?'
Sai suka tattauna a junansu, suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama ne,’ zai ce, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’
32 Or should we say, 'human?'" They were afraid of the people; for all agreed in holding John to have been really a Prophet.
In kuma muka ce, ‘Daga wurin mutane ne’; suna jin tsoron mutane, don kowa ya ɗauka cewa, Yohanna, annabi ne na gaskiya.”
33 So they answered Jesus, "We do not know." "Nor do I tell you," said Jesus, "by what authority I do these things."
Saboda haka, suka amsa wa Yesu suka ce, “Ba mu sani ba.” Yesu ya ce, “To, ni ma ba zan gaya muku ko da wane iko nake yin waɗannan abubuwa ba.”