< 2 Corinthians 5 >

1 For we know that if this poor tent, our earthly house, is taken down, we have in Heaven a building which God has provided, a house not built by human hands, but eternal. (aiōnios g166)
Mun san cewa idan wannan gidan da muke zaune a ciki ya rushe, muna da wani ginin daga wurin Allah. Gida ne wanda ba hannuwan mutane suka gina ba, amma madawwamin gida ne a cikin sama. (aiōnios g166)
2 For in this one we sigh, because we long to put on over it our dwelling which comes from Heaven--
Domin a cikin wannan jiki muna gurnani, muna jira a suturta mu da wurin zaman mu na samaniya.
3 if indeed having really put on a robe we shall not be found to be unclothed.
Muna jiran wannan ne domin ta wurin suturtar da mu ba za a same mu tsirara ba.
4 Yes, we who are in this tent certainly do sigh under our burdens, for we do not wish to lay aside that with which we are now clothed, but to put on more, so that our mortality may be absorbed in Life.
Gama babu shakka yayinda muke cikin wannan alfarwa, muna gurnani, muna nawaita. Ba mu so muyi zaman hutanci. Maimakon haka, muna so a suturtar da mu, domin rai ya hadiye abu mai mutuwa.
5 And He who formed us with this very end in view is God, who has given us His Spirit as a pledge and foretaste of that bliss.
Wanda kuwa yake shirya mu domin ainihin wannan abu Allah ne, wanda ya ba mu Ruhu a matsayin alkawarin abinda ke zuwa.
6 We have therefore a cheerful confidence. We know that while we are at home in the body we are banished from the Lord;
Domin wannan mu zama da gabagadi koyaushe. Mu lura da cewa yayinda muka shagala cikin jiki, muna nesa da Ubangiji.
7 for we are living a life of faith, and not one of sight.
Gama bisa ga bangaskiya muke tafiya, ba bisa ga ganin ido ba.
8 So we have a cheerful confidence, and we anticipate with greater delight being banished from the body and going home to the Lord.
Don haka muna da gabagadi. Mun gwammace mu rabu da jiki domin mu zauna tare da Ubangiji.
9 And for this reason also we make it our ambition, whether at home or in exile, to please Him perfectly.
Sai muka maishe shi burinmu, ko muna cikin jiki ko nesa, mu gamshe shi.
10 For we must all of us appear before Christ's judgement-seat in our true characters, in order that each may then receive an award for his actions in this life, in accordance with what he has done, whether it be good or whether it be worthless.
Domin tilas dukanmu mu hallara a gaban kursiyin shari'a na Almasihu, saboda kowa ya karbi sakamakon abubuwan da yayi cikin jiki, ko masu kyau ne ko marasa kyau.
11 Therefore, because we realize how greatly the Lord is to be feared, we are endeavouring to win men over, and God recognizes what our motives are, and I hope that you, in your hearts, recognize them too.
Don haka, domin mun san tsoron Ubangiji, muna rinjayar mutane. Allah na ganin yadda muke a fili. Ina fatan hakan a fili take ga lamirinku.
12 We are not again commending ourselves to your favour, but are furnishing you with a ground of boasting on our behalf, so that you may have a reply ready for those with whom superficial appearances are everything and sincerity of heart counts for nothing.
Ba muna kokarin mu rinjaye ku domin ku kalle mu a matsayin amintattun mutane ba. Maimakon haka, muna ba ku dalilin yin takama da mu, domin ku sami amsar da za ku bada ga wadanda ke fahariya da kasancewarsu amma ba game da abinda ke zuciya ba.
13 For if we have been beside ourselves, it has been for God's glory; or if we are now in our right senses, it is in order to be of service to you.
Gama idan mun fita daga hankulanmu, saboda Allah ne. Kuma idan muna cikin hankalinmu, domin ku ne.
14 For the love of Christ overmasters us, the conclusion at which we have arrived being this--that One having died for all, His death was their death,
Domin kaunar Almasihu ta tilas ta mu, domin mun tabbatar da wannan: cewa mutum daya ya mutu domin kowa, kuma domin wannan duka sun mutu.
15 and that He died for all in order that the living may no longer live to themselves, but to Him who died for them and rose again.
Kuma Almasihu ya mutu domin kowa, domin wadanda ke raye kada su sake rayuwa domin kansu. A maimakon haka, su yi rayuwa domin shi wanda ya mutu kuma aka tashe shi.
16 Therefore for the future we know no one simply as a man. Even if we have known Christ as a man, yet now we do so no longer.
Domin wannan dalili, daga yanzu ba za mu kara shar'anta kowa bisa ga ma'aunin 'yan'adam ba, ko da yake a baya mun taba duban Almasihu a haka. Amma yanzu mun daina shar'anta kowa ta haka.
17 So that if any one is in Christ, he is a new creature: the old state of things has passed away; a new state of things has come into existence.
Saboda haka, duk wanda ke cikin Almasihu, sabon halitta ne. Tsofaffin al'amura sun shude. Duba, sun zama sababbi.
18 And all this is from God, who has reconciled us to Himself through Christ, and has appointed us to serve in the ministry of reconciliation.
Dukan wadannan abubuwa daga Allah ne. Ya sulhunta mu da kansa ta wurin Almasihu, ya kuma ba mu hidimar sulhu.
19 We are to tell how God was in Christ reconciling the world to Himself, not charging men's transgressions to their account, and that He has entrusted to us the Message of this reconciliation.
Wato, cikin Almasihu, Allah na sulhunta duniya zuwa gare shi, ba tare da lissafin zunubansu a kansu ba. Yana damka mana sakon sulhu.
20 On Christ's behalf therefore we come as ambassadors, God, as it were, making entreaty through our lips: we, on Christ's behalf, beseech men to be reconciled to God.
Don haka an zabe mu a matsayin wakilan Almasihu, kamar dai Allah na kira ga mutane ta wurin mu. Muna rokon ku, saboda Almasihu: ''ku sulhuntu ga Allah!''
21 He has made Him who knew nothing of sin to be sin for us, in order that in Him we may become the righteousness of God.
Shi ya maida Almasihu ya zama hadaya domin zunubinmu. Shine wanda bai taba zunubi ba. Ya yi haka ne don mu zama adalchin Allah a cikin sa.

< 2 Corinthians 5 >