< 1 John 3 >
1 See what marvellous love the Father has bestowed upon us--that we should be called God's children: and that is what we are. For this reason the world does not recognize us--because it has not known Him.
Dubi irin kaunar da Allah ya bamu, har da za a kira mu 'ya'yan Allah, haka muke kuwa. Saboda wannan dalili ne duniya bata san muba, saboda bata san shi ba.
2 Dear friends, we are now God's children, but what we are to be in the future has not yet been fully revealed. We know that if Christ reappears we shall be like Him, because we shall see Him as He is.
Kaunatattu, yanzu mu 'ya'yan Allahne, kuma ba a bayyana mana yadda zamu zama ba tukuna, mun sani sa'adda Almasihu zai bayyana, zamu zama kamarsa, domin zamu ganshi kamar yadda yake.
3 And every man who has this hope fixed on Him, purifies himself so as to be as pure as He is.
Dukkan wanda yake da wannan bege game da gidan gobe ya kan tsarkake kansa, kamar yadda shima yake da tsarki.
4 Every one who is guilty of sin is also guilty of violating Law; for sin is the violation of Law.
Dukkan wanda yaci gaba da yin zunubi yana ketare shari'a kenan. Gama zunubi ketare shari'a ne.
5 And you know that He appeared in order to take away sins; and in Him there is no sin.
Kun sani Almasihu ya bayyana domin ya dauke zunubai ne. Kuma a cikinsa babu zunubi.
6 No one who continues in union with Him lives in sin: no one who lives in sin has seen Him or knows Him.
Ba wanda zai kasance a cikinsa da zai cigaba da yin zunubi. Ba wanda zai ci gaba da aikata zunubi da zai ce ya sanshi, ko kuma ya ganshi.
7 Dear children, let no one lead you astray. The man who acts righteously is righteous, just as He is righteous.
'Ya'yana kaunatattu, kada ku bari kowa ya baudar da ku, wanda yake aikata adalci shi adali ne, kamar yadda Almasihu yake adali.
8 He who is habitually guilty of sin is a child of the Devil, because the Devil has been a sinner from the very beginning. The Son of God appeared for the purpose of undoing the work of the Devil.
Wanda yake aikata zunubi na ibilis ne, gama ibilis yayi zunubi tun daga farko. Dalilin haka ne Dan Allah ya bayyana, domin ya rushe ayyukan ibilis.
9 No one who is a child of God is habitually guilty of sin. A God-given germ of life remains in him, and he cannot habitually sin--because he is a child of God.
Duk wanda aka haife shi daga Allah ba ya yin zunubi, saboda irin Allah na cikinsa. Ba zaya iya ci gaba da yin zunubi ba domin an haife shi daga wurin Allah.
10 By this we can distinguish God's children and the Devil's children: no one who fails to act righteously is a child of God, nor he who does not love his brother man.
Ta haka ne ake bambanta 'ya'yan Allah da 'ya'yan ibilis. Dukkan wanda baya aikata adalci ba na Allah bane; haka kuma wanda ba ya kaunar dan'uwansa.
11 For this is the Message you have heard from the beginning--that we are to love one another.
Domin wannan shine sakon da kuka ji tun daga farko: cewa mu kaunaci junanmu,
12 We are not to resemble Cain, who was a child of the Evil one and killed his own brother. And why did he kill him? Because his own actions were wicked and his brother's actions righteous.
ba kamar Kayinu ba wanda yake na shaidan kuma ya kashe dan'uwansa. Me yasa ya kashe shi? Saboda ayyukansa miyagu ne, na dan'uwansa kuma masu adalci ne.
13 Do not be surprised, brethren, if the world hates you.
Kada kuyi mamaki 'yan'uwana, idan duniya ta ki ku.
14 As for us, we know that we have already passed out of death into Life--because we love our brother men. He who is destitute of love continues dead.
Mun sani mun ratsa mutuwa zuwa cikin rai, saboda muna kaunar 'yan'uwa. Dukkan wanda ba ya yin kauna, shi matacce ne.
15 Every one who hates his brother man is a murderer; and you know that no murderer has the Life of the Ages continuing in him. (aiōnios )
Dukkan wanda yake kin dan'uwansa, mai kisan kai ne. Kun kuma sani babu rai na har abada a cikin mai kisankai. (aiōnios )
16 We know what love is--through Christ's having laid down His life on our behalf; and in the same way we ought to lay down our lives for our brother men.
Ta wurin haka muka san kauna, da ya ke Almasihu ya bayar da ransa saboda mu. Mu ma ya kamata mu bada ranmu saboda 'yan'uwamu.
17 But if any one has this world's wealth and sees that his brother man is in need, and yet hardens his heart against him--how can such a one continue to love God?
Amma duk wanda yake da kayan duniya, ya ga dan'uwansa cikin bukata, kuma bai ji tausayinsa ba, ta yaya kaunar Allah ke cikinsa?
18 Dear children, let us not love in words only nor with the lips, but in deed and in truth.
'Ya'yana kaunatattu, kada muyi kauna ta fatar baki kawai, amma muyi aikin kauna da gaskiya.
19 And in this way we shall come to know that we are loyal to the truth, and shall satisfy our consciences in His presence
Ta wurin haka mun sani mu masu gaskiya ne kuma mun tabbatar da zuciyarmu a gabansa.
20 in whatever matters our hearts condemn us--because God is greater than our hearts and knows everything.
Gama idan zuciyarmu bata kayar damu ba, Allah ya fi zuciyarmu girma, kuma yana sane da kome.
21 Dear friends, if our hearts do not condemn us, we have perfect confidence towards God;
Kaunatattu, idan zuciyarmu bata kashe mu ba, muna da gabagadi a gaban Allah.
22 and whatever we ask for we obtain from Him, because we obey His commands and do the things which are pleasing in His sight.
Kuma duk abin da muka nema zamu samu a wurinsa, saboda muna kiyaye dokokinsa, muna yin abubuwan da suka gamshe shi.
23 And this is His command--that we are to believe in His Son Jesus Christ and love one another, just as He has commanded us to do.
Kuma ummurninsa kenan: mu bada gaskiya ga sunan Dansa Yesu Almasihu, mu yi kaunar juna kuma kamar yanda ya bamu wannan doka.
24 The man who obeys His commands continues in union with God, and God continues in union with him; and through His Spirit whom He has given us we can know that He continues in union with us.
Duk wanda yake kiyaye umarnin Allah, yana cikinsa, Allah kuma yana cikin mutumin. Ta haka muka gane cewa yana cikinmu, Ta wurin Ruhu, wanda ya bamu.