< Song of Solomon 8 >

1 O that thou [wert] as my brother, that was nourished at the breasts of my mother! [when] I should find thee without, I would kiss thee; yes, I should not be despised.
Da a ce kai ɗan’uwa ne gare ni, wanda nonon mahaifiyata sun shayar! Da in na same ka a waje, na sumbace ka, babu wanda zai rena ni.
2 I would lead thee, [and] bring thee into my mother's house, [who] would instruct me: I would cause thee to drink of spiced wine of the juice of my pomegranate.
Da sai in bi da kai in kawo ka gidan mahaifiyata, ita da ta koyar da ni. Da na ba ka ruwan inabi gaurayayye da kayan yaji ka sha, zaƙin rumman nawa.
3 His left hand [should be] under my head, and his right hand should embrace me.
Hannunsa na hagu yana a ƙarƙashin kaina, hannunsa na dama kuma ya rungume ni.
4 I charge you, O daughters of Jerusalem, that ye stir not, nor awake [my] love, until he please.
’Yan matan Urushalima, ku yi mini alkawari. Ba za ku tā da ko ku farka ƙauna ba sai haka ya zama lalle.
5 Who [is] this that cometh up from the wilderness, leaning upon her beloved? I raised thee up under the apple-tree: there thy mother brought thee forth: there she brought thee forth [that] bore thee.
Wace ce wannan da take haurawa daga hamada tana dogara a kan ƙaunataccenta? Ƙaunatacciya A ƙarƙashin itacen gawasa na farkar da ke, a wurin da aka haife ki, wurin da mahaifiyarki ta haife ki.
6 Set me as a seal upon thy heart, as a seal upon thy arm: for love [is] strong as death; jealousy [is] cruel as the grave: the coals of it [are] coals of fire, [which hath] a most vehement flame. (Sheol h7585)
Ka sa ni kamar hatimi a zuciyarka, kamar hatimi a hannunka; gama ƙauna tana da ƙarfi kamar mutuwa, kishinta yana kamar muguntar kabari, yana ƙuna kamar wuta mai ci, kamar gagarumar wuta. (Sheol h7585)
7 Many waters cannot quench love, neither can the floods drown it: if a man would give all the substance of his house for love, it would utterly be contemned.
Ruwa da yawa ba zai iya kashe ƙauna ba, koguna ba za su iya kwashe ta ba. In wani zai bayar da dukan dukiyar gidansa don ƙauna, za a yi masa dariya ne kawai.
8 We have a little sister, and she hath no breasts: what shall we do for our sister in the day when she shall be spoken for?
Muna da ƙanuwa, nonanta ba su riga sun yi girma ba. Me za mu yi da ƙanuwarmu a ranar da za a yi maganar sonta?
9 If she [is] a wall, we will build upon her a palace of silver: and if she [is] a door, we will inclose her with boards of cedar.
Da a ce ita katanga ce, da sai mu gina hasumiyar azurfa a kanta. Da a ce ita ƙofa ce, da sai mun yi mata ƙyauren itacen al’ul.
10 I [am] a wall, and my breasts like towers: then was I in his eyes as one that found favor.
Ni katanga ce kuma nonaina sun yi kamar hasumiya. Ta haka na zama idanunsa kamar wanda yake kawo gamsuwa.
11 Solomon had a vineyard at Baal-hamon; he let out the vineyard to keepers; every one for the fruit of it was to bring a thousand [pieces] of silver.
Solomon ya kasance da gonar inabi a Ba’al-Hamon; ya ba da hayar gonar inabi ga’yan haya. Kowanne zai biya shekel dubu na azurfa don’ya’yan inabin.
12 My vineyard which [is] mine, [is] before me: thou, O Solomon, [must have] a thousand, and those that keep the fruit of it two hundred.
Amma gonar inabina nawa ne da zan bayar; shekel dubu naka ne, ya Solomon, kuma ɗari biyu na waɗanda suke lura da’ya’yan itatuwansa ne.
13 Thou that dwellest in the gardens, the companions hearken to thy voice: cause me to hear [it].
Ke da kike zaune a cikin lambu da ƙawaye suna lura da ke, bari in ji muryarki!
14 Make haste, my beloved, and be thou like a roe or a young hart upon the mountains of spices.
Ka zo, ƙaunataccena, ka zama kamar barewa ko kuwa kamar’yar batsiya a kan dutsen da kayan yaji suke a shimfiɗe.

< Song of Solomon 8 >