< Revelation 5 >

1 And I saw in the right hand of him that sat on the throne a book written within and on the backside, sealed with seven seals.
Sa'annan na ga a cikin hannun daman wanda ke zaune a kan kursiyin, na ga littafi wanda ke da rubutu ciki da waje, an kuma hatimce shi da hatimai bakwai.
2 And I saw a strong angel proclaiming with a loud voice, Who is worthy to open the book, and to loose its seals?
Na kuma ga wani kakkarfan mala'ika na shela da murya mai karfi, “Wa ya isa ya bude littafin ya kuma bambare hatimin?”
3 And no man in heaven, nor in earth, neither under the earth, was able to open the book, neither to look upon it.
Ba wani a sama ko a kasa ko karkashin kasa da ya iya ya bude littafin ko ya karanta abin da ke cikinsa.
4 And I wept much, because no man was found worthy to open, and to read the book, neither to look upon it.
Na yi kuka mai zafi saboda ba wani da ya cancanta da zai bude littafin ko ya karanta abin da ke cikinsa.
5 And one of the elders saith to me, Weep not: behold, the Lion of the tribe of Judah, the Root of David, hath prevailed to open the book, and to loose its seven seals.
Amma daya daga cikin dattawan nan ya ce mani, “Kada ka yi kuka. Duba! Zaki na kabilar Yahuza, Tushen Dauda, ya yi nasara. Ya cancanci bude littafin da kuma hatimansa bakwai.”
6 And I beheld, and lo, in the midst of the throne, and of the four living beings, and in the midst of the elders stood a Lamb as it had been slain, having seven horns, and seven eyes, which are the seven Spirits of God sent forth into all the earth.
Na ga Dan Rago yana tsaye tsakanin kursiyin da rayayyun halittun nan guda hudu a cikin dattawa. Yana kama da wanda aka kashe. Yana da kafonni bakwai da idanuwa bakwai; wadannan sune ruhohin Allah bakwai da aka aiko zuwa dukan duniya.
7 And he came and took the book out of the right hand of him that sat upon the throne.
Ya tafi ya karbi littafin daga hannun daman wanda ke zaune bisa kursiyin.
8 And when he had taken the book, the four living beings, and four [and] twenty elders fell down before the Lamb, having every one of them harps, and golden vials full of odors, which are the prayers of saints.
Lokacin da Dan Ragon ya dauki littafin, rayayyun halittun nan hudu da dattawan nan ashirin da hudu suka fadi har kasa a gaban Dan ragon. Kowannen su na dauke da molo da tasar zinariya cike da kayan kamshi, wadanda kuwa sune addu'o'in masu ba da gaskiya.
9 And they sung a new song, saying, Thou art worthy to take the book, and to open the seals of it: for thou wast slain, and hast redeemed us to God by thy blood out of every kindred, and language, and people, and nation;
Suka raira sabuwar waka: “Ka cancanta ka dauki littafinka kuma bude hatimansa. Domin an yanka ka, da jininka ka saya wa Allah mutane daga kowacce kabila, harshe, jama'a da al'umma.
10 And hast made us to our God kings and priests: and we shall reign on the earth.
Ka maishe su mulki da firistoci su bauta wa Allanmu, kuma za su yi mulki a duniya.”
11 And I beheld, and I heard the voice of many angels around the throne, and the living beings, and the elders: and the number of them was ten thousand times ten thousand, and thousands of thousands;
Da na duba sai na ji karar mala'iku masu yawa kewaye da kursiyin da rayayyun halitu da kuma dattawa. Jimillarsu ya kai dubbai goma, sau dubbai goma, da dubun dubbai.
12 Saying with a loud voice, Worthy is the Lamb that was slain to receive power, and riches, and wisdom, and strength, and honor, and glory, and blessing.
Suka tada murya da karfi suka ce, “Macancanci ne Dan Ragon da aka yanka ya karbi iko, wadata, hikima, karfi, girma, daukaka da yabo.”
13 And every creature which is in heaven, and on the earth, and under the earth, and such as are in the sea, and all that are in them, I heard saying, Blessing, and honor, and glory, and power, [be] to him that sitteth upon the throne, and to the Lamb for ever and ever. (aiōn g165)
Na ji kowanne halittaccen abu da ke cikin sama da kasa da karkashin kasa da cikin teku - dukan abubuwan da ke cikinsu - na cewa, “Ga shi wanda ke zaune a kan kursiyin da kuma Dan Ragon, yabo, girma, daraja, da kuma ikon yin mulki, har abada abadin. (aiōn g165)
14 And the four living beings said, Amen. And the four [and] twenty elders fell down and worshiped him that liveth for ever and ever.
Sai rayayyun halittun nan hudu suka ce, “Amin!” dattawan nan kuma suka fadi da fuskokinsu suka yi sujada.

< Revelation 5 >