< Psalms 49 >
1 To the chief Musician, A Psalm for the sons of Korah. Hear this, all [ye] people; give ear, all [ye] inhabitants of the world:
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
2 Both low and high, rich and poor together.
babba da yaro mai arziki da talaka.
3 My mouth shall speak of wisdom; and the meditation of my heart [shall be] of understanding.
Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
4 I will incline my ear to a parable: I will open my dark saying upon the harp.
Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
5 Why should I fear in the days of evil, [when] the iniquity of my heels shall encompass me?
Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
6 They that trust in their wealth, and boast themselves in the multitude of their riches;
waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
7 None [of them] can by any means redeem his brother, nor give to God a ransom for him:
Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
8 (For the redemption of their soul [is] precious, and it ceaseth for ever: )
kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
9 That he should still live for ever, [and] not see corruption.
da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
10 For he seeth [that] wise men die, likewise the fool and the brutish person perish, and leave their wealth to others.
Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
11 Their inward thought [is], [that] their houses [shall continue] for ever, [and] their dwelling places to all generations; they call [their] lands after their own names.
Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
12 Nevertheless man [being] in honor abideth not: he is like the beasts [that] perish.
Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
13 This their way [is] their folly: yet their posterity approve their sayings. (Selah)
Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
14 Like sheep they are laid in the grave; death shall feed on them; and the upright shall have dominion over them in the morning; and their beauty shall consume in the grave from their dwelling. (Sheol )
Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol )
15 But God will redeem my soul from the power of the grave: for he shall receive me. (Selah) (Sheol )
Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol )
16 Be not thou afraid when one is made rich, when the glory of his house is increased;
Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
17 For when he dieth he shall carry nothing away: his glory shall not descend after him.
gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
18 Though while he lived he blessed his soul: and [men] will praise thee, when thou doest well to thyself.
Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
19 He shall go to the generation of his fathers; they shall never see light.
zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
20 Man [that is] in honor, and understandeth not, is like the beasts [that] perish.
Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.