< Psalms 41 >
1 To the chief Musician, A Psalm of David. Blessed [is] he that considereth the poor: the LORD will deliver him in the time of trouble.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
2 The LORD will preserve him, and keep him alive; [and] he shall be blessed upon the earth: and thou wilt not deliver him to the will of his enemies.
Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
3 The LORD will strengthen him upon the bed of languishing: thou wilt make all his bed in his sickness.
Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
4 I said, LORD, be merciful to me: heal my soul; for I have sinned against thee.
Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
5 My enemies speak evil of me, When shall he die, and his name perish?
Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
6 And if he cometh to see [me], he speaketh vanity: his heart gathereth iniquity to itself; [when] he goeth abroad, he telleth [it].
Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
7 All that hate me whisper together against me: against me do they devise my hurt.
Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
8 An evil disease, [say they], cleaveth fast to him: and [now] that he lieth he shall rise no more.
“Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
9 Yes, my own familiar friend, in whom I trusted, who ate of my bread, hath lifted up [his] heel against me.
Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
10 But thou, O LORD, be merciful to me, and raise me up, that I may requite them.
Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
11 By this I know that thou favorest me, because my enemy doth not triumph over me.
Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
12 And as for me, thou upholdest me in my integrity, and settest me before thy face for ever.
Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
13 Blessed [be] the LORD God of Israel from everlasting, and to everlasting. Amen, and amen.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.