< Psalms 34 >

1 [A Psalm] of David, when he changed his behavior before Abimelech; who drove him away, and he departed. I will bless the LORD at all times: his praise [shall] continually [be] in my mouth.
Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
2 My soul shall make her boast in the LORD: the humble shall hear [of it] and be glad.
Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
3 O magnify the LORD with me, and let us exalt his name together.
Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
4 I sought the LORD, and he heard me, and delivered me from all my fears.
Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
5 They looked to him, and were lightened: and their faces were not ashamed.
Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
6 This poor man cried, and the LORD heard [him], and saved him out of all his troubles.
Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
7 The angel of the LORD encampeth around them that fear him, and delivereth them.
Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
8 O taste and see that the LORD [is] good: blessed [is] the man [that] trusteth in him.
Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
9 O fear the LORD, ye his saints: for [there is] no want to them that fear him.
Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
10 The young lions do lack, and suffer hunger: but they that seek the LORD shall not want any good [thing].
Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
11 Come, ye children, hearken to me; I will teach you the fear of the LORD.
Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
12 What man [is he that] desireth life, [and] loveth [many] days, that he may see good?
Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
13 Keep thy tongue from evil, and thy lips from speaking guile.
ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
14 Depart from evil, and do good; seek peace, and pursue it.
Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
15 The eyes of the LORD [are] upon the righteous, and his ears [are open] to their cry.
Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
16 The face of the LORD [is] against them that do evil, to cut off the remembrance of them from the earth.
fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
17 [The righteous] cry, and the LORD heareth, and delivereth them out of all their troubles.
Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
18 The LORD [is] nigh to them that are of a broken heart; and saveth such as are of a contrite spirit.
Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
19 Many [are] the afflictions of the righteous: but the LORD delivereth him out of them all.
Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
20 He keepeth all his bones: not one of them is broken.
yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
21 Evil shall slay the wicked: and they that hate the righteous shall be desolate.
Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
22 The LORD redeemeth the soul of his servants: and none of them that trust in him shall be desolate.
Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.

< Psalms 34 >