< Psalms 16 >

1 Michtam of David. Preserve me, O God: for in thee do I put my trust.
Miktam ne na Dawuda. Ka kiyaye ni, ya Allah, gama a cikinka nake samun mafaka.
2 [O my soul], thou hast said to the LORD, Thou [art] my LORD: my goodness [extendeth] not to thee;
Na ce wa Ubangiji, “Kai ne shugabana; in ba tare da kai ba, ba ni da wani abu mai kyau.”
3 [But] to the saints that [are] in the earth, and [to] the excellent, in whom [is] all my delight.
Game da tsarkakan da suke cikin ƙasar kuwa, su ne masu ɗaukakar da dukan farin cikina ya dangana.
4 Their sorrows shall be multiplied [that] hasten [after] another [god]: their drink-offerings of blood will I not offer, nor take their names into my lips.
Baƙin ciki zai ƙaru wa waɗanda suke bin waɗansu alloli. Ba zan zuba musu hadayarsu ta jini ba ko in ambaci sunayensu da bakina.
5 The LORD [is] the portion of my inheritance and of my cup: thou maintainest my lot.
Ubangiji, ka ba ni rabona da kwaf ɗin na; ka kiyaye rabona,
6 The lines have fallen to me in pleasant [places]; yes, I have a goodly heritage.
Iyakoki sun fāɗo mini a wurare masu daɗi; tabbatacce ina da gādo mai bansha’awa.
7 I will bless the LORD, who hath given me counsel: my reins also instruct me in the night season.
Zan yabi Ubangiji, wanda yake ba ni shawara; ko da dare ma zuciyata kan koya mini.
8 I have set the LORD always before me: because [he is] at my right hand, I shall not be moved.
Kullum nakan sa Ubangiji a gabana. Gama yana a hannun damana, ba zan jijjigu ba.
9 Therefore my heart is glad, and my glory rejoiceth: my flesh also shall rest in hope.
Saboda haka zuciyata tana murna harshena kuma yana farin ciki; jikina kuma zai zauna lafiya,
10 For thou wilt not leave my soul in hell; neither wilt thou suffer thy Holy One to see corruption. (Sheol h7585)
domin ba za ka yashe ni a kabari ba, ba kuwa za ka bar Mai Tsarkinka yă ruɓa ba. (Sheol h7585)
11 Thou wilt show me the path of life: in thy presence [is] fullness of joy; at thy right hand [are] pleasures for evermore.
Ka sanar da ni hanyar rai; za ka cika ni da farin ciki a gabanka, da madawwamin jin daɗi a hannun damarka.

< Psalms 16 >