< Psalms 110 >

1 A Psalm of David. The LORD said to my Lord, Sit thou at my right hand, until I make thy enemies thy footstool.
Ta Dawuda. Zabura ce. Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”
2 The LORD will send the rod of thy strength out of Zion: rule thou in the midst of thy enemies.
Ubangiji zai fadada ikon sandan mulkinka daga Sihiyona za ka yi mulki a tsakiyar abokan gābanka.
3 Thy people [shall be] willing in the day of thy power, in the beauties of holiness: from the womb of the morning, thou hast the dew of thy youth.
Rundunarka za su so yin yaƙi a ranarka ta yaƙi. Saye cikin ɗaukaka mai tsarki, daga cikin ciki na safiya za ka karɓi raɓar ƙuruciyarka.
4 The LORD hath sworn, and will not repent, Thou [art] a priest for ever after the order of Melchisedek.
Ubangiji ya rantse ba zai kuma canja zuciyarsa ba, “Kai firist ne har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
5 The LORD at thy right hand will strike through kings in the day of his wrath.
Ubangiji yana a hannun damanka; zai murƙushe sarakuna a ranar fushinsa.
6 He will judge among the heathen, he will fill [the places] with the dead bodies; he will wound the heads over many countries.
Zai hukunta al’ummai, yana tarawa gawawwaki yana kuma murƙushe masu mulkin dukan duniya.
7 He will drink of the brook in the way: therefore will he lift up the head.
Zai sha daga rafin da yake kusa da hanya; saboda haka zai ɗaga kansa sama.

< Psalms 110 >