< Matthew 8 >
1 When he had come down from the mountain, great multitudes followed him.
Da ya sauko daga dutsen, sai taron mutane mai yawan gaske suka bi shi.
2 And behold, there came a leper and worshiped him, saying, Lord, if thou wilt, thou canst make me clean.
Wani mutum mai kuturta ya zo ya durƙusa a gabansa ya ce, “Ubangiji, in kana so, kana iya tsabtacce ni.”
3 And Jesus put forth [his] hand, and touched him, saying, I will; be thou clean. And immediately his leprosy was cleansed.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin. Ya ce, “Ina so, ka tsabtacce!” Nan da nan aka warkar da shi daga kuturtarsa.
4 And Jesus saith to him, See thou tell no man; but go, show thyself to the priest, and offer the gift that Moses commanded, for a testimony to them.
Sai Yesu ya ce masa, “Ka lura kada ka gaya wa kowa. Sai dai ka tafi, ka nuna kanka ga firist ka kuma yi bayarwar da Musa ya umarta, a matsayin shaida gare su.”
5 And when Jesus had entered into Capernaum, there came to him a centurion, beseeching him,
Da Yesu ya shiga Kafarnahum, sai wani jarumi ya zo wurinsa, yana neman taimako.
6 And saying, Lord, my servant lieth at home sick with the palsy, grievously tormented.
Ya ce, “Ubangiji, bawana yana kwance a gida shanyayye, yana kuma shan azaba ƙwarai.”
7 And Jesus saith to him, I will come and heal him.
Yesu ya ce masa, “Zan je in warkar da shi.”
8 The centurion answered and said, Lord, I am not worthy that thou shouldst come under my roof: but speak the word only, and my servant will be healed.
Jarumin ya amsa, “Ubangiji, ban cancanci in sa ka zo gidana ba, ka dai yi magana kawai, bawana zai warke.
9 For I am a man under authority, having soldiers under me: and I say to this [man], Go, and he goeth; and to another, Come, and he cometh; and to my servant, Do this, and he doeth [it].
Gama ni kaina mutum ne a ƙarƙashin iko, da kuma sojoji a ƙarƙashina. Nakan ce wa wannan, ‘Je ka,’ sai yă tafi; wancan kuma, ‘Zo nan,’ sai yă zo. Nakan ce wa bawana, ‘Yi wannan,’ sai kuwa yă yi.”
10 When Jesus heard [it], he marveled, and said to them that followed, Verily I say to you, I have not found so great faith, no, not in Israel.
Da Yesu ya ji wannan, sai ya yi mamaki ya kuma ce wa waɗanda suke binsa, “Gaskiya nake gaya muku, ban taɓa samun wani a Isra’ila da bangaskiya mai girma haka ba.
11 And I say to you, that many shall come from the east and the west, and shall sit down with Abraham, and Isaac, and Jacob in the kingdom of heaven.
Ina kuma gaya muku da yawa za su zo daga gabas da kuma yamma, su ɗauki wuraren zamansu a biki tare da Ibrahim, Ishaku, da Yaƙub a cikin mulkin sama.
12 But the children of the kingdom shall be cast out into utter darkness: there shall be weeping and gnashing of teeth.
Amma za a jefar da’ya’yan mulki waje, zuwa cikin baƙin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.”
13 And Jesus said to the centurion, Depart; and as thou hast believed, so be it done to thee. And his servant was healed in the same hour.
Sa’an nan Yesu ya ce wa jarumin, “Je ka! Za a yi bisa ga bangaskiyarka.” A daidai wannan lokaci bawansa kuwa ya warke.
14 And when Jesus had come into Peter's house, he saw his wife's mother laid, and sick with a fever.
Da Yesu ya zo cikin gidan Bitrus, sai ya ga surukar Bitrus tana kwance a gado tana da zazzaɓi.
15 And he touched her hand, and the fever left her: and she arose, and ministered to them.
Ya taɓa hannunta sai zazzaɓin ya sake ta, ta kuwa tashi ta fara yin masa hidima.
16 When the evening was come, they brought to him many that were possessed with demons: and he cast out the spirits with [his] word, and healed all that were sick;
Da yamma ta yi, aka kawo masa masu aljanu da yawa, ya kuwa fitar da ruhohin ta wurin magana, ya kuma warkar da dukan marasa lafiya.
17 That it might be fulfilled which was spoken by Isaiah the prophet, saying, He himself took our infirmities, and bore [our] sicknesses.
Wannan ya faru ne domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya cewa, “Ya ɗebi rashin lafiyarmu, ya kuma ɗauki cututtukanmu.”
18 Now when Jesus saw great multitudes about him, he gave commandment to depart to the other side.
Da Yesu ya ga taron mutane kewaye da shi, sai ya ba da umarni a ƙetare zuwa ɗayan hayin tafkin.
19 And a certain scribe came, and said to him, Master, I will follow thee whithersoever thou goest.
Sai wani malamin dokoki ya zo wurinsa ya ce, “Malam, zan bi ka duk inda za ka.”
20 And Jesus saith to him, The foxes have holes, and the birds of the air [have] nests; but the Son of man hath not where to lay [his] head.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Yanyawa suna da ramummuka, tsuntsayen sararin sama suna da sheƙuna, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin da zai sa kansa.”
21 And another of his disciples said to him, Lord, suffer me first to go and bury my father.
Sai wani almajiri ya ce masa, “Ubangiji, da farko bari in je in binne mahaifina.”
22 But Jesus said to him, Follow me; and let the dead bury their dead.
Amma Yesu ya ce masa, “Ka bi ni, ka bar matattu su binne matattunsu.”
23 And when he had entered into a boat, his disciples followed him.
Sai ya shiga jirgin ruwa, almajiransa kuwa suka bi shi.
24 And behold, there arose a great tempest in the sea, insomuch that the boat was covered with the waves: but he was asleep.
Ba zato ba tsammani, sai wani babban hadari ya taso a tafkin, har raƙuman ruwan suka sha kan jirgin. Amma Yesu yana barci.
25 And his disciples came to [him], and awoke him, saying, Lord, save us: we perish.
Almajiran suka je suka tashe shi, suna cewa, “Ubangiji, ka cece mu! Za mu nutse!”
26 And he saith to them, Why are ye fearful, O ye of little faith? Then he arose, and rebuked the winds and the sea; and there was a great calm.
Ya amsa ya ce, “Ku masu ƙarancin bangaskiya, me ya sa kuke tsoro haka?” Sa’an nan ya tashi ya tsawata wa iskar da kuma raƙuman ruwan, sai wuri ya yi tsit gaba ɗaya.
27 But the men marveled, saying, What manner of man is this, that even the winds and the sea obey him!
Mutanen suka yi mamaki suka ce, “Wane irin mutum ne wannan? Har iska da raƙuman ruwa suna masa biyayya!”
28 And when he had come to the other side, into the country of the Gergesenes, there met him two possessed with demons, coming out of the tombs, exceeding fierce, so that no man might pass by that way.
Da ya isa ɗayan gefen a yankin Gadarenawa (ko kuwa Gerasenawa), sai ga mutum biyu masu aljanu suna fitowa daga kaburbura suka tarye shi. Su abin tsoro ne ƙwarai, har ba mai iya bin wannan hanya.
29 And behold, they cried out, saying, What have we [to do] with thee, Jesus, [thou] Son of God? art thou come hither to torment us before the time?
Suka yi ihu suka ce, “Me ya haɗa ka da mu, Ɗan Allah?” Ka zo ne nan don ka ji mana kafin lokaci yă yi?
30 And there was a good way off from them a herd of many swine, feeding.
Nesa kaɗan da su kuwa akwai babban garken aladu da yake kiwo.
31 So the demons besought him, saying, If thou expellest us, suffer us to go away into the herd of swine.
Aljanun suka roƙi Yesu suka ce, “In ka fitar da mu, tura mu cikin garken aladun nan.”
32 And he said to them, Go. And when they had come out, they went into the herd of swine: and behold, the whole herd of swine ran violently down a steep place into the sea, and perished in the waters.
Ya ce musu, “Ku tafi!” Sai suka fita suka shiga cikin aladun, dukan garken kuwa ya gangara a guje daga kan tudun zuwa cikin tafkin aladun kuma suka mutu a cikin ruwa.
33 And they that kept them, fled, and went into the city, and told every thing; and what had befallen to the possessed with demons.
Masu kiwon aladun suka ruga, suka je cikin gari suka ba da labarin dukan wannan, haɗe da abin da ya faru da mutanen nan masu aljanu.
34 And behold, the whole city came out to meet Jesus: and when they saw him, they besought him that he would depart out of their borders.
Sai dukan garin suka fito don su taryi Yesu. Da suka kuwa gan shi, sai suka roƙe shi yă bar musu yanki.