< Matthew 24 >
1 And Jesus went out, and departed from the temple: and his disciples came to [him] to show him the buildings of the temple.
Yesu ya bar haikali ke nan, yana cikin tafiya sai almajiransa suka zo wurinsa don su ja hankalinsa ga gine-ginen haikali.
2 And Jesus said to them, See ye not all these things? verily I say to you, There shall not be left here one stone upon another, that shall not be thrown down.
Sai Yesu ya ce, “Kun ga duk waɗannan abubuwa? Gaskiya nake gaya muku, ba wani dutse a nan da za a bari a kan wani; duk za a rushe.”
3 And as he sat upon the mount of Olives, the disciples came to him privately, saying, Tell us, when will these things be? and what [will be] the sign of thy coming, and of the end of the world? (aiōn )
Da Yesu yana zaune a Dutsen Zaitun, almajiran suka zo wurinsa a ɓoye. Suka ce, “Gaya mana, yaushe ne wannan zai faru, mece ce alamar zuwanka da kuma ta ƙarshen zamani?” (aiōn )
4 And Jesus answered and said to them, Take heed that no man deceive you.
Yesu ya amsa, “Ku lura fa, kada wani yă ruɗe ku.
5 For many will come in my name, saying, I am Christ; and will deceive many.
Gama mutane da yawa za su zo cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne Kiristi,’ za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
6 And ye will hear of wars, and rumors of wars: see that ye be not troubled: for all [these things] must come to pass, but the end is not yet.
Za ku ji labarin yaƙe-yaƙe da kuma jita-jitarsu, sai dai ku lura kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru, amma ƙarshen tukuna.
7 For nation will rise against nation, and kingdom against kingdom: and there will be famines, and pestilences, and earthquakes in divers places.
Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki yă tasar wa mulki. Za a yi yunwa da girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam.
8 All these [are] the beginning of sorrows.
Dukan waɗannan fa, mafarin azabar naƙudar haihuwa ne.
9 Then will they deliver you up to be afflicted, and will kill you: and ye will be hated by all nations for my name's sake.
“Sa’an nan za a bashe ku don a tsananta muku a kuma kashe ku, dukan al’ummai za su ƙi ku saboda ni.
10 And then will many be offended, and will betray one another, and will hate one another.
A wannan lokaci, da yawa za su juya daga bangaskiya, su ci amana su kuma ƙi juna,
11 And many false prophets will rise, and will deceive many.
annabawan ƙarya da yawa za su firfito su kuma ruɗi mutane da yawa.
12 And because iniquity will abound, the love of many will become cold.
Saboda ƙaruwar mugunta, ƙaunar yawanci za tă yi sanyi,
13 But he that shall endure to the end, the same shall be saved.
amma duk wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
14 And this gospel of the kingdom shall be preached in all the world, for a testimony to all nations; and then shall the end come.
Za a kuma yi wa’azin wannan bisharar mulki a cikin dukan duniya, yă zama shaida ga dukan al’ummai, sa’an nan ƙarshen yă zo.
15 When therefore ye shall see the abomination of desolation spoken of by Daniel the prophet, stand in the holy place, (whoever readeth, let him understand, )
“Saboda haka sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama mai kawo hallaka,’wanda annabi Daniyel ya yi magana a kai, yana tsaye a tsattsarkan wuri (mai karatu yă gane),
16 Then let them who are in Judea flee to the mountains:
to, sai waɗanda suke cikin Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu.
17 Let him who is on the house-top not come down to take any thing out of his house:
Kada wani da yake a kan rufin gidansa, yă sauko don ɗaukar wani abu a gida.
18 Neither let him who is in the field return back to take his clothes.
Kada wani da yake gona kuma yă komo don ɗaukar rigarsa.
19 And woe to them that are with child, and to them that nurse infants in those days!
Kaiton mata masu ciki da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
20 But pray ye that your flight may not be in the winter, neither on the sabbath:
Ku yi addu’a, kada gudunku yă zama a lokacin sanyi ko a ranar Asabbaci.
21 For then shall be great tribulation, such as hath not been since the beginning of the world to this time, no, nor ever shall be.
Gama a lokacin za a yi wata matsananciyar wahala, wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu ba kuwa za a ƙara yi ba.
22 And except those days should be shortened, there would no flesh be saved: but for the elect's sake those days shall be shortened.
“Da ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da babu wani da zai tsira, amma saboda zaɓaɓɓun nan, za a taƙaita kwanakin.
23 Then if any man shall say to you, Lo, here [is] Christ, or there; believe [it] not.
A lokacin in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko, ‘Ga shi can!’ Kada ku gaskata.
24 For false Christs will arise, and false prophets, and will show great signs and wonders; so that, if [it were] possible, they would deceive the very elect.
Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
25 Behold, I have told you before.
Ga shi, na faɗa muku tun da wuri.
26 Wherefore, if they shall say to you, Behold, he is in the desert; go not forth: behold, [he is] in the secret chambers; believe [it] not.
“Saboda haka in wani ya ce muku, ‘Ga shi can a hamada,’ kada ku fita; ko, ‘Ga shi nan a ɗakunan ciki,’ kada ku gaskata.
27 For as the lightning cometh out of the east, and shineth even to the west; so shall also the coming of the Son of man be.
Gama kamar yadda walƙiya take wulgawa walai daga gabas zuwa yamma, haka dawowar Ɗan Mutum zai kasance.
28 For wherever the carcass is, there will the eagles be collected.
Duk inda mushe yake, can ungulai za su taru.
29 Immediately after the tribulation of those days, shall the sun be darkened, and the moon shall not give her light, and the stars shall fall from heaven, and the powers of the heavens shall be shaken:
“Nan da nan bayan tsabar wahalan nan “‘sai a duhunta rana, wata kuma ba zai ba da haskensa ba; taurari kuma za su fāffāɗi daga sararin sama, za a kuma girgiza abubuwan sararin sama.’
30 And then shall appear the sign of the Son of man in heaven: and then shall all the tribes of the earth mourn, and they shall see the Son of man coming in the clouds of heaven with power and great glory.
“A sa’an nan ne alamar dawowar Ɗan Mutum zai bayyana a sararin sama, dukan al’umman duniya kuwa za su yi kuka. Za su ga Ɗan Mutum yana zuwa kan gizagizan sararin sama, da iko da kuma ɗaukaka mai girma.
31 And he will send his angels with a great sound of a trumpet, and they will gather his elect from the four winds, from one end of heaven to the other.
Zai kuwa aiki mala’ikunsa su busa ƙaho mai ƙara sosai, za su kuwa tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga wannan bangon duniya zuwa wancan.
32 Now learn a parable of the fig-tree; When its branch is yet tender and putteth forth leaves, ye know that summer [is] nigh:
“Yanzu fa, sai ku koyi wannan darasi daga itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi ganyayensa kuma suka toho, kun san damina ta kusa.
33 So likewise ye, when ye shall see all these things, know that it is near, [even at] the doors.
Haka kuma, sa’ad da kun ga dukan waɗannan abubuwa, ku sani ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
34 Verily I say to you, This generation shall not pass, till all these things shall be fulfilled.
Gaskiya nake gaya muku, wannan zamani ba zai shuɗe ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
35 Heaven and earth shall pass away, but my words shall not pass away.
Sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za tă taɓa shuɗe ba.
36 But of that day and hour knoweth no [man], no, not the angels of heaven, but my Father only.
“Babu wanda ya san wannan rana ko sa’a, ko mala’ikun da suke sama ma, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai.
37 But as the days of Noah [were], so will also the coming of the Son of man be.
Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
38 For as in the days that were before the flood, they were eating and drinking, marrying and giving in marriage, until the day that Noah entered into the ark,
Gama a kwanaki kafin ruwan tsufana, mutane sun yi ta ci, sun kuma yi ta sha, suna aure, suna kuma aurarwa, har zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi;
39 And knew not until the flood came, and took them all away: so also will be the coming of the Son of man.
ba su kuwa san abin da yake faruwa ba sai da ruwan tsufana ya zo ya share su tas. Haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
40 Then will two be in the field; the one shall be taken, and the other left.
Maza biyu za su kasance a gona; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
41 Two [women will be] grinding at the mill; the one shall be taken, and the other left.
Mata biyu za su kasance suna niƙa; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
42 Watch therefore; for ye know not what hour your Lord cometh.
“Saboda haka sai ku zauna a faɗake, gama ba ku san a wace rana ce Ubangijinku zai zo ba.
43 But know this, that if the master of the house knew in what watch the thief would come, he would watch, and would not suffer his house to be broken up.
Ku dai gane wannan, da maigida ya san ko a wane lokaci ne da dare, ɓarawo zai zo, da sai yă zauna a faɗake yă kuma hana a shiga masa gida.
44 Therefore be ye also ready: for in such an hour as ye think not, the Son of man cometh.
Saboda haka ku ma, sai ku zauna a faɗake, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku za tă ba.
45 Who then is a faithful and wise servant, whom his Lord hath made ruler over his household, to give them food in due season?
“Wane ne bawan nan mai aminci da kuma mai hikima, wanda maigida ya sa yă lura da bayi a cikin gidansa, yă riƙa ba su abinci a daidai lokaci?
46 Blessed [is] that servant, whom his lord, when he cometh, shall find so doing.
Zai zama wa bawan nan da kyau in maigidan ya dawo ya same shi yana yin haka.
47 Verily I say to you, that he will make him ruler over all his goods.
Gaskiya nake gaya muku, zai sa shi yă lura da dukan dukiyarsa.
48 But if that evil servant shall say in his heart, My Lord delayeth his coming;
Amma in wannan bawa mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Maigidana ba zai dawo da wuri ba.’
49 And shall begin to beat [his] fellow-servants, and to eat and drink with the drunken;
Sa’an nan yă fara dūkan’yan’uwansa bayi, yana ci yana kuma sha tare da mashaya.
50 The Lord of that servant will come in a day when he looketh not for [him], and in an hour that he is not aware of,
Maigidan wannan bawa zai dawo a ranar da bai yi tsammani ba, a sa’ar kuma da bai sani ba.
51 And will cut him asunder, and appoint [him] his portion with the hypocrites: there shall be weeping and gnashing of teeth.
Maigidan zai farfasa masa jiki da bulala, yă kuma ba shi wuri tare da munafukai, inda za a yi kuka da cizon haƙora.