< Matthew 22 >
1 And Jesus answered, and spoke to them again by parables, and said,
Yesu ya sake yi masu magana da misalai, yace,
2 The kingdom of heaven is like to a certain king, who made a marriage for his son,
“Mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya shirya wa dansa liyafar aure.
3 And sent his servants to call them that were invited to the wedding: and they would not come.
Ya aiki bayinsa su kira wadanda aka gayyata su zo liyafar auren, amma suka ki zuwa.
4 Again, he sent other servants, saying, Tell them who are invited, Behold, I have prepared my dinner: my oxen and [my] fatlings [are] killed, and all things [are] ready: come to the marriage.
Sai sarkin ya sake aiken wasu bayin, yace, “Ku gaya wa wadanda aka gayyata, “Duba, na shirya liyafata. An yanka bajimaina da kosassun 'yanmarukana, an gama shirya komai. Ku zo wurin bikin auren.”
5 But they made light of [it], and went, one to his farm, another to his merchandise.
Amma mutanen ba su dauki sakon da mahimmanci ba kuma suka yi tafiyarsu. Wani ga gonarsa, wani ga kasuwancinsa.
6 And the remnant took his servants, and treated [them] spitefully, and slew [them].
Sauran kuma suka kama bayin sarkin, suka wulakanta su, suka kuma kashe su.
7 But when the king heard [of it], he was wroth: and he sent his armies, and destroyed those murderers, and burned up their city.
Amma sarkin ya ji haushi. Ya aika sojojinsa, ku kashe masu kisan kan nan, ku kuma kone birnin su.
8 Then he saith to his servants, The wedding is ready, but they who were invited were not worthy.
Sai ya ce wa bayinsa, 'An gama shirya bikin, amma wadanda aka gayyata ba su cancanta ba.
9 Go ye therefore into the highways, and as many as ye shall find, invite to the marriage.
Saboda haka ku je bakin hanya ku gayyaci iyakar yawan mutanen da za ku samu zuwa bukin auren.'
10 So those servants went out into the highways, and collected all as many as they found, both bad and good: and the wedding was furnished with guests.
Bayin suka tafi hanya suka tattaro dukan mutanen da suka samu, da masu kyau da marassa kyau. Zauren auren kuwa ya cika makil da baki.
11 And when the king came in to see the guests, he saw there a man who had not a wedding-garment:
Amma da sarkin ya zo don ya ga bakin, sai ya ga wani wanda bai sa kayan aure ba.
12 And he saith to him, Friend, how camest thou in hither, not having a wedding-garment? And he was speechless.
Sai sarkin ya ce masa, 'Aboki, ta yaya ka shigo nan ba tare da kayan aure ba?' Mutumin kuwa ya rasa ta cewa.
13 Then said the king to the servants, Bind him hand and foot, and take him away, and cast [him] into utter darkness: there shall be weeping and gnashing of teeth.
Sai sarkin ya ce wa bayinsa, 'Ku daure mutumin nan hannu da kafa, ku jefa shi cikin duhun, inda za ayi kuka da cizon hakora.'
14 For many are called, but few [are] chosen.
Gama mutane dayawa aka kira, amma kadan aka zaba.”'
15 Then went the Pharisees, and took counsel how they might entangle him in [his] talk.
Sai Farisawan suka tafi suka shirya makirci akan yadda zasu kama shi ta maganarsa.
16 And they sent out to him their disciples, with the Herodians, saying, Master, we know that thou art true, and teachest the way of God in truth, neither carest thou for any [man]: for thou regardest not the person of men.
Suka tura masa almajiransu, da Hirudiyawa. Suka ce ma Yesu, “Mallam, mun san kai mai gaskiya ne, kuma kana koyar da hanyar Ubangiji da gaskiya. Ba ka damu da ra'ayin kowa ba, kuma ba ka nuna bambanci a tsakanin mutane.
17 Tell us therefore, What thinkest thou? Is it lawful to give tribute to Cesar, or not?
To gaya mana, menene tunaninka? Ya halarta a biya haraji ga Kaisar ko a'a?”
18 But Jesus perceived their wickedness, and said, Why tempt ye me, [ye] hypocrites?
Amma Yesu ya gane muguntarsu yace, “Don me kuke gwada ni, ku munafukai?
19 Show me the tribute-money. And they brought to him a penny.
Ku nuna mani sulen harajin.” Sai suka kawo masa sulen.
20 And he saith to them, Whose [is] this image, and superscription?
Yesu yace masu, “Hoto da sunan wanene wadannan?”
21 They say to him, Cesar's. Then saith he to them, Render therefore to Cesar, the things which are Cesar's; and to God, the things that are God's.
Suka ce masa, “Na Kaisar.” Sai Yesu ya ce masu, “To ku ba Kaisar abubuwan dake na Kaisar, Allah kuma abubuwan dake na Allah.”
22 When they had heard [these words], they marveled, and left him, and departed.
Da suka ji haka, suka yi mamaki. Sai suka bar shi suka tafi.
23 The same day came to him the Sadducees, who say that there is no resurrection, and asked him,
A ran nan sai wadansu Sadukiyawa, wadanda suka ce ba tashin matattu, suka zo wurinsa. Suka tambaye shi,
24 Saying, Master, Moses said, If a man shall die, having no children, his brother shall marry his wife, and raise up seed to his brother.
cewa, “Mallam, Musa yace, 'Idan mutum ya mutu, bashi da 'ya'ya, dole dan'uwansa ya auri matarsa ya kuwa haifawa dan'uwansa 'ya'ya.
25 Now there were with us seven brothers: and the first, when he had married a wife, deceased; and having no issue, left his wife to his brother.
Akwai wasu 'yan'uwa bakwai. Na farkon yayi aure sai ya mutu. Da shike bai bar 'ya'ya ba. Ya bar wa dan'uwansa matarsa.
26 Likewise the second also, and the third, to the seventh.
Sai dan'uwansa na biyu shi ma yayi haka, haka kuma na ukun, har zuwa dan'uwan na bakwai.
27 And last of all the woman died also.
Bayan dukansu, sai matar ta mutu.
28 Therefore in the resurrection, whose wife shall she be of the seven? for they all had her.
To a tashin matattu, matar wa zata zama a cikin su bakwai din? Don duk sun aure ta.”
29 Jesus answered and said to them, Ye do err, not knowing the scriptures, nor the power of God.
Amma Yesu ya amsa yace masu, “Kun bata, domin ba ku san litattafai ko ikon Allah ba.
30 For in the resurrection they neither marry, nor are given in marriage, but are as the angels of God in heaven.
Domin a tashin matattu basu aure, ba kuma a bada su aure. Maimaikon haka, suna kama da mala'ikun sama.
31 But as concerning the resurrection of the dead, have ye not read that which was spoken to you by God, saying,
Amma game da tashin matattu, ba ku karanta abinda Allah ya fada maku ba, cewa,
32 I am the God of Abraham, and the God of Isaac, and the God of Jacob? God is not the God of the dead, but of the living.
'Nine Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku, da Allah na Yakubu'? Allah ba Allah na matattu bane, amma na rayayyu.”
33 And when the multitude heard [this], they were astonished at his doctrine.
Da taron suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.
34 But when the Pharisees had heard that he had put the Sadducees to silence, they were assembled about him.
Amma da Farisawan suka ji cewa Yesu ya kure Sadukiyawa, sai suka tattara kansu.
35 Then one of them [who was] a lawyer, asked [him a question], tempting him, and saying,
Daya daga cikinsu, masanin shari'a, yayi masa tambaya, yana gwada shi-
36 Master, which [is] the great commandment in the law?
“Mallam, wace doka ce mafi girma a cikin shari'a?”
37 Jesus said to him, Thou shalt love the Lord thy God with all thy heart, and with all thy soul, and with all thy mind.
Yesu yace masa, “Ka kaunaci Ubangiji Allahnka da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka, da dukkan hankalinka.'
38 This is the first and great commandment.
Wannan itace babbar doka ta farko.
39 And the second [is] like it, Thou shalt love thy neighbor as thyself.
Doka ta biyu kuma kamar ta take- 'Ka kaunaci makwabcinka kamar kanka.'
40 On these two commandments hang all the law and the prophets.
Akan wadannan dokoki ne dukkan shari'a da annabawa suka rataya.”
41 While the Pharisees were assembled, Jesus asked them,
Yayin da Farisawa suke tattare wuri daya, Yesu yayi masu tambaya.
42 Saying, What think ye of Christ? whose son is he? They say to him, [The son] of David.
Yace, “Me kuke tunani game da Almasihu? Shi dan wanene?” Suka ce masa, ''Dan Dauda ne.”
43 He saith to them, How then doth David in spirit call him Lord, saying,
Yesu yace masu, “To ta yaya kuma Dauda cikin Ruhu ya kira shi Ubangiji, yana cewa,
44 The LORD said to my Lord, Sit thou on my right hand, till I make thy enemies thy footstool?
“Ubangiji ya cewa wa Ubangijina, zauna a hannun damana, har sai na mai da makiyanka matakin sawayenka.”
45 If David then calleth him Lord, how is he his son?
Idan Dauda ya kira Almasihu 'Ubangiji,' ta yaya ya zama dan Dauda?”
46 And no man was able to answer him a word, neither durst any [man], from that day forth, ask him any more questions.
Ba wanda ya iya bashi amsa, ba kuma wanda ya kara yi masa tambayoyi tun daga wannan rana.