< Matthew 21 >
1 And when they drew nigh to Jerusalem, and had come to Bethphage, to the mount of Olives, then Jesus sent two disciples,
Yayinda Yesu da almajiransa suka kusato Urushalima sai suka zo Betafaji wajen dutsen zaitun, sai Yesu ya aiki almajiransa guda biyu,
2 Saying to them, Go into the village over against you, and immediately ye shall find an ass tied, and a colt with her, loose [them], and bring [them] to me.
yace masu, “Ku shiga kauyen da yake gaban ku zaku iske wata jaka da aholaki tara da ita. Ku kwance su ku kawo mani su.
3 And if any [man] shall say aught to you, ye shall say, The Lord hath need of them; and immediately he will send them.
Idan wani ya gaya maku wani abu game da haka, sai ku ce, 'Ubangiji ne yake bukatarsu,' mutumin kuwa zai aiko ku da su nan da nan.”
4 All this was done, that it might be fulfilled which was spoken by the prophet, saying,
Anyi wannan kuwa domin a cika annabcin anabin. Yace,
5 Tell ye the daughter of Sion, Behold, thy King cometh to thee, meek, and sitting upon an ass, and a colt the foal of an ass.
“Ku cewa diyar Sihiyona, duba, ga sarkinki na zuwa wurin ki, mai tawali'u ne, kuma akan jaki wanda aholaki ne.”
6 And the disciples went, and did as Jesus commanded them,
Sai almajiran suka tafi suka yi kamar yadda Yesu ya umarce su.
7 And brought the ass and the colt, and put on them their clothes, and they set [him] thereon.
Suka kawo jakar da dan aholakin, suka sa tufafinsu akai, Yesu kuwa ya zauna akan tufafin.
8 And a very great multitude spread their garments in the way; others cut down branches from the trees, and strewed [them] in the way.
Yawancin jama'a kuwa suka baza tufafinsu akan hanya, wasu kuma suka yanko ganye daga bishiyoyi suka shimfida su a hanya.
9 And the multitudes that went before, and that followed, cried, saying, Hosanna to the son of David: blessed [is] he that cometh in the name of the Lord: Hosanna in the highest.
Taron jama'a da suke gabansa da wadanda suke bayansa, suka ta da murya suna cewa, “Hossana ga dan Dauda! mai albarka ne shi wanda ke zuwa cikin sunan Ubangiji. Hossana ga Ubangiji!”
10 And when he had come into Jerusalem, all the city was moved, saying, Who is this?
Sa'adda Yesu ya shiga Urushalima sai doki ya cika birnin ana cewa, “Wanene wannan?”
11 And the multitude said, This is Jesus the prophet of Nazareth of Galilee.
Sai jama'a suka amsa, “Wannan shine Yesu annabi, daga Nazaret ta Galili.”
12 And Jesus went into the temple of God, and cast out all them that sold and bought in the temple, and overthrew the tables of the money-changers, and the seats of them that sold doves.
Sai Yesu ya shiga haikalin. Ya kori duk wadanda ke saye da sayarwa a cikin ikiilisiya. Ya birkice teburan masu canjin kudi da kujerun masu sayar da tantabaru.
13 And said to them, It is written, My house shall be called the house of prayer, but ye have made it a den of thieves.
Ya ce masu, “A rubuce yake, 'Za a kira gidana gidan addu'a,' amma kun mayar dashi kogon 'yan fashi.”
14 And the blind and the lame came to him in the temple; and he healed them.
Sai makafi da guragu suka zo wurin sa a haikalin, ya warkar da su.
15 And when the chief priests and scribes saw the wonderful things that he did, and the children crying in the temple, and saying, Hosanna to the son of David; they were greatly displeased,
Amma da manyan firistoci da malaman attaura suka ga abubuwan banmamaki da yayi, kuma sa'adda suka ji yara suna tada murya a cikin haikalin suna cewa, “Hossana ga dan Dauda,” sai suka ji haushi.
16 And said to him, Hearest thou what these say? And Jesus saith to them, Yes: have ye never read, Out of the mouth of babes and sucklings thou hast perfected praise?
Suka ce masa, kana jin abinda wadannan mutanen ke fadi?'' Yesu ya ce masu, “I! Amma ba ku taba karantawa ba, 'daga bakin jarirai da masu shan mama ka sa yabo'?”
17 And he left them, and went out of the city into Bethany, and he lodged there.
Sai Yesu ya bar su, ya fice daga birnin zuwa Betaniya ya kwana a wurin.
18 Now in the morning as he was returning into the city, he was hungry.
Washegari da safe yayin da yake komawa birnin, sai yaji yunwa.
19 And when he saw a fig-tree in the way, he came to it, and found nothing on it, but leaves only, and said to it, Let no fruit grow on thee henceforth for ever. And immediately the fig-tree withered. (aiōn )
Da ya ga bishiyar baure a bakin hanya, sai yaje wurin amma bai sami kome ba sai dai ganye. Sai ya ce mata, “Kada ki kara yin 'ya'ya har abada.” Sai nan take bishiyar bauren ta bushe. (aiōn )
20 And when the disciples saw [it], they marveled, saying, How soon is the fig-tree withered!
Da almajiran suka ga haka, sai suka yi mamaki suka ce, “Kaka bishiyar bauren ta bushe nan da nan?”
21 Jesus answered and said to them, Verily I say to you, If ye have faith, and doubt not, ye shall not only do this [which is done] to the fig-tree, but also, if ye shall say to this mountain, Be thou removed, and be thou cast into the sea; it shall be done.
Yesu ya amsa yace masu, “Hakika ina ce maku, in dai kuna da bangaskiya ba ku yi shakka ba, ba abinda aka yi wa bauren nan kadai za kuyi ba har ma za ku cewa tsaunin nan, “Ka ciru ka fada teku,' sai kuwa haka ta kasance.
22 And all things whatever ye shall ask in prayer, believing, ye shall receive.
Kome kuka roka cikin addu'a, in dai kun gaskanta, za ku samu.”
23 And when he had come into the temple, the chief priests and the elders of the people came to him as he was teaching, and said, By what authority doest thou these things; and who gave thee this authority?
Sa'adda Yesu ya shiga haikalin, sai manyan fristocin da shugabannin jama'a suka zo suka same shi yayin da yake koyarwa, suka ce, “Da wane iko kake yin wadannan abubuwa?”
24 And Jesus answered and said to them, I also will ask you one thing, which if ye tell me, I also will tell you by what authority I do these things.
Yesu ya amsa yace masu, “Ni ma zan yi maku tambaya daya. In kun fada mani, ni ma zan fada maku ko da wane iko nake yin wadannan abubuwa.
25 The baptism of John, whence was it? from heaven, or from men? And they reasoned with themselves, saying, if we shall say, From heaven; he will say to us, Why then did ye not believe him?
Daga ina baftismar Yahaya ta fito, daga sama ko kuma daga mutune?” Sai suka yi shawara a tsakanin su, suka ce, “In munce, 'daga sama,' zai ce mana, 'don me bamu gaskanta dashi ba?'
26 But if we shall say, From men; we fear the people: for all hold John as a prophet.
Amma in munce, ' daga mutune,' muna tsoron jama'a, saboda sun san Yahaya annabi ne.”
27 And they answered Jesus, and said, We cannot tell. And he said to them, Neither do I tell you by what authority I do these things.
Sai suka amsa ma Yesu suka ce, ''Bamu sani ba.” Shi ma yace masu, “Nima bazan gaya maku ko da wane iko nake yin abubuwan nan ba.
28 But what think ye? A [certain] man had two sons; and he came to the first, and said, Son, go, work to-day in my vineyard.
Amma me kuke tunani? Wani mutum yana da 'ya'ya biyu. Ya je wurin na farkon yace, 'Da, je ka kayi aiki yau a cikin gona.'
29 He answered and said, I will not; but afterward he repented, and went.
Yaron ya amsa yace, 'bazan yi ba,' amma daga baya ya canza tunaninsa ya tafi.
30 And he came to the second, and said likewise. And he answered and said, I [go], sir: and went not.
Sai mutumin ya je wurin da na biyun ya fada masa abu guda. Wannan dan ya amsa ya ce, 'zanje, baba,' amma bai je ba.
31 Which of the two did the will of [his] father? They say to him, The first. Jesus saith to them, Verily I say to you, that the publicans and the harlots go into the kingdom of God before you.
Wanene a cikin 'ya'ya biyun nan yayi nufin ubansa?” Suka ce, “na farkon.” Yesu ya ce masu, “Hakika ina gaya maku, masu karbar haraji da karuwai za su shiga mulkin Allah kafin ku.
32 For John came to you in the way of righteousness, and ye believed him not: but the publicans and the harlots believed him: and ye, when ye had seen [it], repented not afterward, that ye might believe him.
Gama Yahaya ya zo maku a hanyar adalci, amma ba ku gaskata da shi ba, a yayinda masu karbar haraji da karuwai suka gaskata da shi. Ku kuwa, bayan kun ga abin da ya faru, baku ma tuba daga baya ba don ku gaskata da shi.
33 Hear another parable; There was a certain householder, who planted a vineyard, and hedged it around, and digged a wine-press in it, and built a tower, and let it out to husbandmen, and went into a remote country:
Ku saurari wani misalin. Anyi wani mutum, mai gona. Yayi shuka a gonar, ya shinge ta, ya gina ramin matse inabi a cikin gonar, ya kuma gina wata hasumiyar tsaro, sai ya bada hayar gonar ga wadansu manoma. Sai ya tafi wata kasa.
34 And when the time of the fruit drew near, he sent his servants to the husbandmen, that they might receive the fruits of it.
Da kakar inabi ta yi, sai ya aiki wadansu bayi su karbo masa amfanin gonar.
35 And the husbandmen took his servants, and beat one, and killed another, and stoned another.
Amma manoman suka kama bayin, suka doddoki dayan, suka kashe dayan, suka jejjefe dayan da duwatsu.
36 Again he sent other servants more than the first: and they did to them in like manner.
Sai mai gonar ya sake aika wadansu bayinsa da suka fi na farko, amma manoman suka yi masu kamar yadda suka yi wa sauran.
37 But last of all he sent to them his son, saying, They will reverence my son.
Bayan wannnan, sai mai gonar ya aika da dansa wurin su yana cewa, 'za su yi wa dana biyayya.'
38 But when the husbandmen saw the son, they said among themselves, This is the heir; come, let us kill him, and let us seize on his inheritance.
Amma da manoman suka ga dan, sai suka ce a tsakanin su, 'wannan shine magajin. Kuzo, mu kashe shi mu gaji gonar.'
39 And they caught him, and cast [him] out of the vineyard, and slew [him].
Sai suka dauke shi, suka jefar da shi daga cikin gonar, suka kashe shi.
40 When therefore the Lord of the vineyard cometh, what will he do to those husbandmen?
To idan me gonar ya zo, me zai yiwa manoman?
41 They say to him, He will miserably destroy those wicked men, and will let out [his] vineyard to other husbandmen, who will render him the fruits in their seasons.
Suka ce masa, “Zai hallaka mugayen manoman nan ta hanya mai tsanani, zai kuma bada gonar haya ga wadansu manoman, mutanen da za su biya, lokacin da inabin ya nuna.”
42 Jesus saith to them, Did ye never read in the scriptures, The stone which the builders rejected, the same is become the head of the corner: this is the Lord's doing, and it is marvelous in our eyes?
Yesu yace masu, “Baku taba karantawa a nassi ba,'' 'Dutsen da magina suka ki ya zama dutse mafi amfani. Wannan daga Ubangijine, kuma abin mamaki ne a idanunmu?'
43 Therefore I say to you, The kingdom of God shall be taken from you, and given to a nation bringing forth the fruits of it.
Saboda haka ina gaya maku, za a karbe mulkin Allah daga wurin ku a ba wata al'umma da zata bada amfaninsa.
44 And whoever shall fall on this stone, shall be broken: but on whomsoever it shall fall, it will grind him to powder.
Duk wanda ya fadi akan dutsen nan zai ragargaje. Amma duk wanda dutsen ya fadawa, zai nike.”
45 And when the chief priests and Pharisees had heard his parables, they perceived that he spoke of them.
Da manyan firistocin da farisawan suka ji wannan misalin, sai suka gane da su yake.
46 But when they sought to lay hands on him, they feared the multitude, because they took him for a prophet.
Da suka nemi kama shi, sai suka ji tsoron taron, saboda mutanen sun dauke shi annabi.