< Matthew 2 >
1 Now, after Jesus was born in Bethlehem of Judea in the days of Herod the king, behold, there came wise men from the east to Jerusalem,
Bayanda aka haifi Yesu a Baitalami ta kasar Yahudiya, a zamanin sarki Hirudus, sai ga wadansu masana daga gabas suka zo Urushalima, suna cewa,
2 Saying, Where is he that is born king of the Jews? for we have seen his star in the east, and have come to worship him.
''Ina wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Mun ga tauraronsa a gabas mun kuma zo mu yi masa sujada.''
3 When Herod the king had heard [these things], he was troubled, and all Jerusalem with him.
Da sarki Hirudus ya ji haka, sai ya damu kwarai, haka kuma dukan mutanen Urushalima.
4 And when he had assembled all the chief priests and scribes of the people, he inquired of them where Christ should be born.
Hirudus ya tara dukan manyan firistoci da marubuta na jama'a, ya tambaye su, “Ina za a haifi Almasihun?”
5 And they said to him, In Bethlehem of Judea: for thus it is written by the prophet,
Suka ce masa, ''A Baitalami ne ta kasar Yahudiya, domin haka annabin ya rubuta,
6 And thou Bethlehem, [in] the land of Judah, art not the least among the princes of Judah: for out of thee shall come a Governor, that shall rule my people Israel.
'Ke kuma, Baitalami, ta kasar Yahudiya, ba ke ce mafi kankanta ba a cikin shugabanin Yahudiya, domin daga cikin ki mai mulki zai fito wanda zai zama makiyayin jama'a ta Isra'ila.'''
7 Then Herod, when he had privately called the wise men, inquired of them diligently what time the star appeared.
Sai Hirudus ya kira masanan a asirce ya tambaye su aininhin lokacin da tauraron ya bayyana.
8 And he sent them to Bethlehem, and said, Go, and search diligently for the young child; and when ye have found [him], bring me word again, that I may come and worship him also.
Ya aike su Baitalami, ya ce, ''Ku je ku binciko mani dan yaron da kyau. Idan kun same shi, ku kawo mani labari, don ni ma in je in yi masa sujada.”
9 When they had heard the king, they departed; and lo, the star, which they saw in the east, went before them, till it came and stood over where the young child was.
Bayan sun ji maganar sarkin, sai suka yi tafiyar su, ga shi kuwa, tauraron da suka gani a gabas yana tafe a gaban su, har ya zo ya tsaya bisa inda dan yaron nan yake.
10 When they saw the star, they rejoiced with exceeding great joy.
Da suka ga tauraron, sai suka yi matukar farin ciki.
11 And when they had come into the house, they saw the young child with Mary his mother, and fell down, and worshiped him: and when they had opened their treasures, they presented to him gifts; gold, and frankincense, and myrrh.
Sai suka shiga gidan, suka ga dan yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka rusuna gabansa suka yi masa sujada. Sa'an nan suka kwance kayansu, suka mika masa kyautar su ta zinariya da lubban, da mur.
12 And being warned by God in a dream that they should not return to Herod, they departed into their own country another way.
Allah kuma ya gargade su a mafarki kada su koma wurin Hirudus, sai suka koma kasarsu ta wata hanya dabam.
13 And when they had departed, behold, the angel of the Lord appeareth to Joseph in a dream, saying, Arise, and take the young child and his mother, and flee into Egypt, and be thou there until I bring thee word: for Herod will seek the young child to destroy him.
Bayan sun tashi, sai ga wani mala'ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusufu a mafarki, ya ce, ''Tashi, ka dauki dan yaron da mahaifiyarsa, ka gudu zuwa kasar Masar, ka zauna a can sai na fada maka, don Hirudus yana shirin binciko dan yaron ya hallaka shi.”
14 When he arose, he took the young child and his mother by night, and departed into Egypt:
A wannan dare fa Yusufu ya tashi ya dauki dan yaron da mahafiyarsa ya tafi Masar.
15 And was there until the death of Herod: that it might be fulfilled which was spoken from the Lord by the prophet, saying, Out of Egypt have I called my son.
Ya zauna a can har mutuwar Hirudus. Wannan kuwa domin a cika abin da Ubangiji ya fada ne ta bakin annabin, ''Daga Masar na kirawo Da na.''
16 Then Herod, when he saw that he was mocked by the wise men, was exceeding wroth, and sent forth, and slew all the children that were in Bethlehem, and in all its borders, from two years old and under, according to the time which he had diligently inquired of the wise men.
Da Hirudus ya ga masanan nan sun shashantar da shi, sai ya hasala kwarai, ya aika a karkashe dukan 'yan yara maza da suke Baitalami da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa kasa, gwargwadon lokacin da ya tabbatar a gun masanan.
17 Then was fulfilled that which was spoken by Jeremiah the prophet, saying,
A lokacin ne aka cika fadar Annabi Irmiya,
18 In Rama was there a voice heard, lamentation, and weeping, and great mourning, Rachel weeping [for] her children, and would not be comforted, because they are not.
''An ji wata murya a Rama, tana kuka da bakin ciki mai zafi, Rahila ce take kuka saboda 'ya'yanta, kuma ta ki ta ta'azantu, domin ba su.
19 But when Herod was dead, behold, an angel of the Lord appeareth in a dream to Joseph in Egypt,
Sa'adda Hirudus ya mutu, sai ga mala'ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusufu a mafarki a Masar ya ce,
20 Saying, Arise, and take the young child and his mother, and go into the land of Israel: for they are dead who sought the young child's life.
''Tashi ka dauki dan yaron da mahaifiyarsa, ka tafi kasar Isra'ila, domin masu neman ran dan yaron sun mutu.''
21 And he arose, and took the young child and his mother, and came into the land of Israel.
Yusufu ya tashi, ya dauki dan yaron da mahaifiyarsa, ya zo kasar Isra'ila.
22 But when he heard that Archelaus reigned in Judea in the room of his father Herod, he was afraid to go thither: notwithstanding, being warned by God in a dream, he turned aside into the parts of Galilee:
Amma da ya ji Arkilayus ya gaji mahaifinsa Hirudus, yana mulkin kasar Yahudiya, sai ya ji tsoron isa can. Bayan da Allah ya yi masa gargadi a mafarki, sai ya ratse zuwa kasar Galili
23 And he came and dwelt in a city called Nazareth: that it might be fulfilled which was spoken by the prophets, He shall be called a Nazarene.
sai ya je ya zauna a wani gari da ake kira Nazarat. Wannan ya cika abin da aka fada ta bakin annabawa, cewa, za a kira shi Banazare.