< Matthew 19 >
1 And it came to pass, [that] when Jesus had finished these sayings, he departed from Galilee, and came into the borders of Judea, beyond Jordan:
Sai ya zama sa'adda Yesu ya gama wadannan maganganu, sai ya bar Galili ya zo kan iyakokin Yahudiya, ketaren kogin Urdun.
2 And great multitudes followed him, and he healed them there.
Taro mai yawa suka bi shi, ya kuma warkar da su a wurin.
3 The Pharisees also came to him, tempting him, and saying to him, Is it lawful for a man to put away his wife for every cause?
Farisawa suka zo wurinsa, suna gwada shi, suka ce masa, ''Ya hallata bisa ga doka mutum ya saki matarsa don kowanne dalili?''
4 And he answered and said to them, Have ye not read, that he who made [them], at the beginning made them male and female,
Yesu ya amsa ya ce, ''Baku karanta ba, cewa shi wanda ya yi su tun farko ya yi su miji da mace?
5 And said, For this [cause] shall a man leave father and mother, and shall cleave to his wife: and they two shall be one flesh?
Shi wanda ya yi su kuma ya ce, “Saboda wannan dalilin, mutum zai rabu da mahaifinsa da mahaifiyarsa ya hade da matarsa, su biyun su zama jiki daya?”
6 Wherefore they are no more two, but one flesh. Therefore what God hath joined together, let not man put asunder.
Su ba biyu ba ne kuma, amma jiki daya. Don haka, duk abin da Allah ya hada, kada wani ya raba.''
7 They say to him, Why did Moses then command to give a writing of divorcement, and to put her away?
Sai suka ce masa, ''To me yasa Musa ya umarcemu mu bada takardar saki, mu kuma kore ta?''
8 He saith to them, Moses, because of the hardness of your hearts, suffered you to put away your wives: but from the beginning it was not so.
Sai ya ce masu, ''Saboda taurin zuciyarku, shi yasa Musa ya yarda maku ku saki matanku, amma da farko ba haka yake ba.
9 And I say to you, Whoever shall put away his wife, except for lewdness, and shall marry another, committeth adultery: and whoever marrieth her who is put away, committeth adultery.
Ina gaya maku, duk wanda ya saki matarsa in ba saboda zina ba, ya kuma auri wata, yana zina kenan. Wanda kuma ya auri macen da aka saka, yana aikata zina.''
10 His disciples say to him, If the case of the man is so with [his] wife, it is not good to marry.
Almajiran suka ce wa Yesu, ''Idan haka yake game da mutum da matarsa, ba kyau ayi aure ba.''
11 But he said to them, All [men] cannot receive this saying, save [they] to whom it is given.
Amma Yesu yace masu, ''Ba kowa ne zai karbi wannan koyarwa ba, amma sai wadanda an yardar masu su karbe ta.
12 For there are some eunuchs, who were so born from [their] mothers womb: and there are some eunuchs, who were made eunuchs by men: and there are eunuchs, who have made themselves eunuchs for the kingdom of heaven's sake. He that is able to receive [it], let him receive [it].
Akwai wadanda aka haife su babanni. Akwai wadanda mutane ne suka maida su babanni. Sa'annan akwai wadanda sun mayar da kansu babanni saboda mulkin sama. Duk wanda zai iya karbar wannan koyarwa, ya karba.''
13 Then were brought to him little children, that he should put [his] hands on them, and pray: and the disciples rebuked them.
Sai aka kawo masa yara kanana don ya dibiya hannuwansa akansu, yayi masu addu'a, amma almajiran suka kwabe su.
14 But Jesus said, Suffer little children, and forbid them not to come to me: for of such is the kingdom of heaven.
Amma Yesu ya ce masu, ''Ku bar yara kanana, kada ku hana su zuwa wuri na, domin mulkin sama na irinsu ne.''
15 And he laid [his] hands on them, and departed thence.
Ya sa hannuwa akan su, sa'annan ya bar wurin.
16 And behold, one came and said to him, Good Master, what good thing shall I do that I may have eternal life? (aiōnios )
Sai wani mutum ya zo wurin Yesu, ya ce, ''Malam, wanne ayyuka nagari ne zan yi domin in sami rai madawwami?'' (aiōnios )
17 And he said to him, Why callest thou me good? [there is] none good but one, [that is], God: but if thou wilt enter into life, keep the commandments.
Yesu ya ce masa, ''Me yasa kake tambaya ta game da abin da ke nagari? Daya ne kawai ke nagari, amma idan kana so ka shiga cikin rai, ka kiyaye dokokin.''
18 He saith to him, Which? Jesus said, Thou shalt do no murder, Thou shalt not commit adultery, Thou shalt not steal, Thou shalt not bear false witness,
Mutumin ya ce masa, ''Wadanne dokokin?'' Yesu ya ce masa, ''Kada kayi kisa, kada kayi zina, kada kayi sata, kada kayi shaidar zur,
19 Honor thy father and [thy] mother: and, Thou shalt love thy neighbor as thyself.
ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, kuma ka kaunaci makwabcinka kamar kanka.''
20 The young man saith to him, All these things have I kept from my youth: what lack I yet?
Saurayin nan ya ce masa, ''Ai na kiyaye duk wadannan. Me nake bukata kuma?''
21 Jesus said to him, If thou wilt be perfect, go [and] sell what thou hast, and give to the poor, and thou shalt have treasure in heaven: and come [and] follow me.
Yesu ya ce masa, ''Idan kana so ka zama cikakke, ka tafi ka sayar da mallakarka, ka kuma ba matalauta, zaka sami dukiya a sama. Sa'annan ka zo ka biyo ni.''
22 But when the young man heard that saying, he went away sorrowful: for he had great possessions.
Amma da saurayin nan ya ji abin da Yesu ya fada, ya koma da bakin ciki, domin shi mai arziki ne kwarai.
23 Then said Jesus to his disciples, Verily I say to you, that a rich man shall with difficulty enter into the kingdom of heaven.
Yesu ya ce wa almajiransa, ''Hakika ina gaya maku, zai zama da wuya mai arziki ya shiga mulkin sama.
24 And again I say to you, It is easier for a camel to go through the eye of a needle, than for a rich man to enter into the kingdom of God.
Ina sake gaya maku, zai fi wa rakumi sauki ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.''
25 When his disciples heard [it], they were exceedingly amazed, saying, Who then can be saved?
Da almajiran sun ji haka, suka yi mamaki kwarai da gaske, suka ce, ''Wanene zai sami ceto?''
26 But Jesus beheld [them], and said to them, With men this is impossible, but with God all things are possible.
Yesu ya dube su, ya ce, ''A wurin mutane wannan ba zai yiwu ba, amma a wurin Allah, kome mai yiwuwa ne.''
27 Then answered Peter, and said to him, Behold, we have forsaken all, and followed thee? what shall we have therefore?
Sai Bitrus ya amsa ya ce masa, ''Duba, mun bar kome da kome mun bi ka. To me za mu samu?''
28 And Jesus said to them, Verily I say to you, that ye who have followed me in the regeneration, when the Son of man shall sit on the throne of his glory, ye also shall sit upon twelve thrones, judging the twelve tribes of Israel.
Yesu ya ce masu, ''Hakika ina gaya maku, ku da kuka bi ni, a sabuwar haihuwa, lokacin da Dan Mutum ya zauna a kursiyin daukakarsa, ku ma zaku zauna a kursiyoyi goma sha biyu, kuna shari'anta kabilu goma sha biyu na Isra'ila.
29 And every one that hath forsaken houses, or brethren, or sisters, or father, or mother, or wife, or children, or lands for my name's sake, shall receive a hundred-fold, and shall inherit everlasting life. (aiōnios )
Duk wanda ya bar gidaje, 'yan'uwa maza, 'yan'uwa mata, mahaifi, mahaifiya, 'ya'ya, ko gonaki, saboda sunana, zai sami ninkin su dari, ya kuma gaji rai madawwami. (aiōnios )
30 But many [that are] first shall be last, and the last [shall be] first.
Amma dayawa dake farko yanzu, za su zama na karshe, dayawa dake karshe kuma, su zama na farko.