< Matthew 15 >
1 Then came to Jesus scribes and Pharisees, who were of Jerusalem, saying,
Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka zo wurin Yesu daga Urushalima suka yi tambaya suka ce,
2 Why do thy disciples transgress the tradition of the elders? for they wash not their hands when they eat bread.
“Me ya sa almajiranka suke karya al’adun dattawa? Ba sa wanke hannuwansu kafin su ci abinci!”
3 But he answered and said to them, Why do ye also transgress the commandment of God by your tradition?
Yesu ya amsa ya ce, “Ku ma me ya sa kuke karya dokar Allah saboda al’adarku?
4 For God commanded, saying, Honor thy father and mother: and, He that curseth father or mother, let him die the death.
Gama Allah ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, kuma duk wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa dole a kashe shi.’
5 But ye say, Whoever shall say to [his] father or [his] mother, [It is] a gift, by whatever thou mightest be profited by me;
Amma ku kukan ce, in wani ya ce wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa, ‘Duk taimakon da dā ya kamata za ku samu daga gare ni an ba wa Allah,’
6 And honor not his father or his mother, [he shall be free]. Thus have ye made the commandment of God of no effect by your tradition.
ba zai ‘girmama mahaifinsa’ da shi ba. Ta haka kun yi banza da maganar Allah saboda al’adarku.
7 [Ye] hypocrites, well did Isaiah prophesy of you, saying,
Ku munafukai! Daidai ne Ishaya ya yi annabci a kanku da ya ce,
8 This people draw nigh to me with their mouth, and honor me with [their] lips; but their heart is far from me.
“‘Waɗannan mutane da baki kawai suke girmama ni, amma zukatansu suna nesa da ni.
9 But in vain they do worship me, teaching [for] doctrines the commandments of men.
A banza suke mini sujada, koyarwarsu, dokoki ne kawai da mutane suke koyarwa.’”
10 And he called the multitude, and said to them, Hear, and understand:
Sai Yesu ya kira taron wurinsa ya ce, “Ku saurara ku kuma gane.
11 Not that which goeth into the mouth defileth a man; but that which cometh out of the mouth, this defileth a man.
Abin da yake shiga bakin mutum ba ya ƙazantar da shi, sai dai abin da yake fitowa daga bakinsa, shi ne yake ƙazantar da shi.”
12 Then came his disciples, and said to him, Knowest thou that the Pharisees were offended after they heard this saying?
Sai almajiran suka zo wurinsa suka ce, “Ka san cewa Farisiyawa ba su ji daɗi sa’ad da suka ji wannan ba?”
13 But he answered and said, Every plant, which my heavenly Father hath not planted, shall be extirpated.
Ya amsa ya ce, “Duk tsiron da Ubana na sama bai shuka ba, za a tumɓuke shi daga saiwoyi.
14 Let them alone: they are blind leaders of the blind. And if the blind leadeth the blind, both will fall into the ditch.
Ku ƙyale su, ai, makafin jagorai ne. In makaho ya yi wa makaho jagora, dukansu za su fāɗa a rami.”
15 Then answered Peter and said to him, Declare to us this parable.
Bitrus ya ce, “Ka bayyana mana wannan misali.”
16 And Jesus said, Are ye also yet without understanding?
Yesu ya tambaye su ya ce, “Har yanzu ba ku gane ba ne?
17 Do ye not yet understand, that whatever entereth in at the mouth goeth into the belly, and is cast out into the draught?
Ba ku gane cewa duk abin da ya shiga baki yakan wuce ciki ne daga nan kuma yă fita daga jiki ba?
18 But those things which proceed out of the mouth come forth from the heart; and they defile the man.
Amma abubuwan da suke fitowa ta baki suna fitowa ne daga zuciya, su ne kuma suke ƙazantar da mutum.
19 For out of the heart proceed evil thoughts, murders, adulteries, fornications, thefts, false witness, blasphemies:
Gama daga zuciya ne mugayen tunani, kisankai, zina, fasikanci, sata, shaidar ƙarya, ɓatan suna, suka fitowa.
20 These are [the things] which defile a man: but to eat with unwashen hands defileth not a man.
Waɗannan su ne suke ƙazantar da mutum; amma cin abinci ba tare da wanke hannuwa ba, ba ya ƙazantar da mutum.”
21 Then Jesus went thence, and departed into the territories of Tyre and Sidon.
Barin wurin ke nan, sai Yesu ya janye zuwa yankin Taya da Sidon.
22 And behold, a woman of Canaan came out of the same territories, and cried to him, saying, Have mercy on me, O Lord, [thou] son of David; my daughter is grievously afflicted with a demon.
Wata mutuniyar Kan’ana daga wajajen ta zo wurinsa, tana ihu tana cewa, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!’Yata tana shan wahala ƙwarai daga aljanin da yake cikinta.”
23 But he answered her not a word. And his disciples came and besought him, saying, Send her away; for she crieth after us.
Yesu bai ce mata uffam ba. Saboda haka almajiransa suka zo wurinsa suka roƙe shi suka ce, “Ka kore ta tă tafi, tana ta binmu tana damunmu da ihu.”
24 But he answered and said, I am not sent but to the lost sheep of the house of Israel.
Ya amsa ya ce, “An aiko ni wurin ɓatattun tumakin Isra’ila ne kaɗai.”
25 Then came she and worshiped him, saying, Lord, help me.
Sai macen ta zo ta durƙusa a gabansa ta ce, “Ubangiji, ka taimake ni!”
26 But he answered and said, It is not meet to take the children's bread, and to cast [it] to dogs.
Ya amsa ya ce, “Ba daidai ba ne a ɗauki abincin yara a jefa wa karnukansu.”
27 And she said, Truth, Lord: yet the dogs eat of the crums which fall from their master's table.
Ta amsa, ta ce, “I, Ubangiji, amma karnuka ma sukan ci gutsattsarin da sukan fāɗi daga teburin maigidansu.”
28 Then Jesus answered and said to her, O woman, great [is] thy faith: be it to thee even as thou wilt. And her daughter was healed from that very hour.
Sa’an nan Yesu ya amsa ya ce, “Mace, kina da bangaskiya mai yawa! An biya miki bukatarki.”’Yarta kuwa ta warke nan take.
29 And Jesus departed from thence, and came nigh to the sea of Galilee; and ascended a mountain, and sat down there.
Yesu ya tashi daga nan ya bi ta gefen Tekun Galili. Sa’an nan ya haura gefen wani dutse ya zauna.
30 And great multitudes came to him, having with them [those that were] lame, blind, dumb, maimed, and many others, and cast them down at Jesus' feet; and he healed them:
Taron mutane mai girma kuwa suka zo wurinsa, suna kawo masa guragu, makafi, shanyayyu, kurame da dai waɗansu da yawa, suka kuwa kwantar da su a gabansa; ya kuma warkar da su.
31 So that the multitude wondered, when they saw the dumb to speak, the maimed to be whole, the lame to walk, and the blind to see: and they glorified the God of Israel.
Mutanen kuwa suka yi mamaki sa’ad da suka ga kurame suna magana, shanyayyu suna samun lafiya, guragu suna takawa, makafi kuma suna ganin gari. Sai suka yabi Allah na Isra’ila.
32 Then Jesus called his disciples [to him], and said, I have compassion on the multitude, because they continue with me now three days, and have nothing to eat: and I will not send them away fasting, lest they faint in the way.
Yesu ya kira almajiransa wurinsa ya ce, “Ina jin tausayin mutanen nan; gama kwana uku ke nan suke tare da ni ba abin da za su ci. Ba na so in sallame su da yunwa, don kada su kāsa a hanya.”
33 And his disciples say to him, Whence should we have so much bread in the wilderness, as to satisfy so great a multitude?
Sai almajiransa suka amsa suka ce, “Ina za mu sami isashen burodi a wannan wurin da babu kowa mu ciyar da irin taron nan?”
34 And Jesus saith to them, How many loaves have ye? And they said, Seven, and a few little fishes.
Yesu ya tambaye su, “Burodi guda nawa kuke da shi?” Suka amsa suka ce, “Guda bakwai da’yan ƙananan kifaye.”
35 And he commanded the multitude to sit on the ground.
Ya sa taron su zazzauna a ƙasa.
36 And he took the seven loaves and the fishes, and gave thanks, and broke [them], and gave to his disciples, and the disciples to the multitude.
Sa’an nan ya ɗauki burodi guda bakwai da kuma kifayen nan, da ya yi godiya, sai ya kakkarya su ya ba wa almajiran, su kuma suka ba wa mutane.
37 And they all ate and were filled: and they took up of the fragments that were left seven baskets full.
Duk kuwa suka ci, suka ƙoshi. Daga baya almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna bakwai.
38 And they that had eaten were four thousand men, besides women and children.
Yawan waɗanda suka ci kuwa, maza dubu huɗu ne, ban da mata da yara.
39 And he sent away the multitude, and took a boat, and came into the borders of Magdala.
Bayan Yesu ya sallami taron, sai ya shiga jirgin ruwa ya tafi wajajen Magadan.