< Mark 14 >

1 After two days was [the feast of] the passover, and of unleavened bread: and the chief priests, and the scribes, sought how they might take him by craft, and put [him] to death.
Idin Ketarewa da bukin gurasa mara yisti sauran kwana biyu kenan, sai shugabanin firistoci da malaman attaura suka nemi yadda zasu kama Yesu a asirce domin su kashe shi.
2 But they said, Not on the feast -[day], lest there should be an uproar of the people.
Suna cewa amma “Ba a lokacin idin ba, domin kada su haddasa hargitsi a tsakanin mutane”.
3 And being in Bethany, in the house of Simon the leper, as he sat at table, there came a woman having an alabaster box of ointment of spikenard, very precious; and she broke the box, and poured [it] on his head.
Yesu yana Betanya a gidan Saminu kuturu, yana shirin liyafa kenan sai ga wata mace dauke da kwalbar turare mai tamanin kwarai, ta shafa masa a kansa.
4 And there were some that had indignation within themselves, and said, Why was this waste of the ointment made?
wasu dake tare da Yesu suka husata, suna kwalbarta da cewa
5 For it might have been sold for more than three hundred pence, and have been given to the poor. And they murmured against her.
“Ai wannan turare ne mai tsada, ina laifin a sayar a raba wa talakawa kudin? ina dalilin wannan almubazaranci?
6 And Jesus said, Let her alone; why trouble ye her? she hath wrought a good work on me.
Sai Yesu yace masu “Ku kyaleta, don me kuke tsauta mata,
7 For ye have the poor with you always, and whenever ye will ye may do them good: but me ye have not always.
ai Idan kuna da niyyar taimakon talakawa ko matalauta, suna nan tare da ku ko a yaushe amma ni bazan kasance da ku kullum ba.
8 She hath done what she could: she is come beforehand to anoint my body to the burying.
Macen nan tayi aiki nagari domin shirya jikina ga jana'iza.
9 Verily I say to you, Wherever this gospel shall be preached throughout the whole world, [this] also that she hath done shall be spoken of, for a memorial of her.
hakika, Ina gaya maku, duk inda za'a yi bishara a duniya baza a mance da matan nan da hidimar da ta tayi mini ba.”
10 And Judas Iscariot, one of the twelve, went to the chief priests, to betray him to them.
Da jin haka sai Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin manzannin ya ruga zuwa wurin baban firist domin ya bashe shi a garesu,
11 And when they heard [it], they were glad, and promised to give him money. And he sought how he might conveniently betray him.
Da mayan firistoci suka ji haka suka yi murna matuka tare da alkawarin kudi ga Yahuza, shi kuwa sai ya fara neman zarafin da zai mika Yesu a gare su.
12 And the first day of unleavened bread, when they killed the passover, his disciples said to him, Where wilt thou that we go and prepare, that thou mayest eat the passover?
A ranar farko ta bukin gurasa marar yisti da kuma hadayar ragon Idin ketarewa, almajiransa suka ce masa “Ina zamu shirya liyafar domin idin ketarewa?
13 And he sendeth two of his disciples, and saith to them, Go ye into the city, and there shall meet you a man bearing a pitcher of water: follow him.
Ya aiki biyu daga cikin almajiransa da cewa “Ku shiga cikin birnin, zaku tarar da wani mutum dauke da tullun ruwa.
14 And wherever he shall go in, say ye to the master of the house, The Master saith, Where is the guest-chamber, where I may eat the passover with my disciples?
Duk gidan da ya shiga ku bishi, sai ku cewa mai gidan, malam yace “ina bukatar masauki domin hidimar idin ketarewa tare da almajiraina?”'
15 And he will show you a large upper room furnished [and] prepared: there make ready for us.
Zai kuwa nuna maku babban bene gyararre. Sai ku yi mana shiri a can.”
16 And his disciples went, and came into the city, and found as he had said to them: and they made ready the passover.
Da shigar almajiran cikin birnin, sai kome ya kasance yadda ya fada, su kuwa suka yi shirye shiryen idin ketarewar.
17 And in the evening he cometh with the twelve.
Da maraice ta yi, sai ya tare da sha biyun.
18 And as they sat, and were eating, Jesus said, Verily I say to you, One of you who eateth with me, will betray me.
Yayin da suke zazzaune a teburin suna cin abincin, sai Yesu ya ce “Hakika ina gaya maku wani da ke ci tare da ni a nan zai bashe ni”.
19 And they began to be sorrowful, and to say to him one by one, [Is] it I? and another [said], [Is] it I?
Sai suka damu suka tambaye shi daya bayan daya suna cewa “Hakika bani bane ko?”
20 And he answered and said to them, [It is] one of the twelve that dippeth with me in the dish.
Yesu ya amsa masu da cewa “Daya daga cikin sha biyu ne, wanda ke sa hannu tare da ni yanzu cikin tasar”.
21 The Son of man indeed goeth, as it is written concerning him: but woe to that man by whom the Son of man is betrayed! good were it for that man if he had never been born.
Dan Mutum zai tafi ne yadda nassi ya umarta game da shi amma kaiton wanda zai bashe shi! “zai, fiye masa, dama ba a haife shi ba”.
22 And as they were eating, Jesus took bread, and blessed, and broke [it], and gave to them, and said, Take, eat: this is my body.
Lokacin da suke cin abincin, Yesu ya dauki gurasa ya sa albarka, ya gutsuttsura ta, sai ya basu yana cewa “Wannan jikinana ne”.
23 And he took the cup, and when he had given thanks, he gave [it] to them: and they all drank of it.
Ya kuma dauki koko, yayi godiya, ya basu, su kuwa suka sha daga kokon.
24 And he said to them, This is my blood of the new testament, which is shed for many.
Ya ce “Wannan jinina ne na alkawari da an zubar ga yawancin mutane”.
25 Verily I say to you, I will drink no more of the fruit of the vine, until that day that I drink it new in the kingdom of God.
Hakika, bazan kara sha daga wannan ruwan inabi ba sai a ranar da zan sha sabo cikin mulkin Allah.”
26 And when they had sung a hymn, they went out to the mount of Olives.
Bayan sun raira wakar yabo ga Allah, sai suka tafi wurin dutsen zaitun.
27 And Jesus saith to them, All ye will be offended because of me this night: for it is written, I will smite the shepherd, and the sheep shall be scattered.
Yesu ya ce masu dukkan ku zaku yi tuntube harma ku fadi saboda ni gama rubuce take cewa “Zan buge makiyayin, tumakin kuwa za su watse;
28 But after that I am risen, I will go before you into Galilee.
Amma bayan tashina, zai yi gaba in riga ku zuwa Galili.
29 But Peter said to him, Although all shall be offended, yet [will] not I.
Bitrus ya ce masa “ko dukkansu sun fadi, faufau banda ni”.
30 And Jesus saith to him, Verily I say to thee, that this day, [even] in this night, before the cock shall crow twice, thou wilt deny me thrice.
Yesu yace masa “Hakika ina gaya maka, cikin wannan dare kafin carar zakara ta biyu zaka yi musun sani na sau uku”.
31 But he spoke the more vehemently, If I should die with thee, I will not deny thee in any wise. Likewise also said they all.
Amma Bitrus ya sake cewa “Koda za'a kasheni tare da kai ba zan yi musun sanin ka ba”. Dukkan su kuwa suka yi wannan Alkawari.
32 And they came to a place which was named Gethsemane: and he saith to his disciples, Sit ye here, while I shall pray.
Suka isa wani wuri da ake kira Getsamani, sai Yesu ya ce wa almajiransa “Ku dakata anan domin zan je inyi addu'a”.
33 And he taketh with him Peter, and James, and John, and began to be greatly amazed, and to be very heavy;
Sai ya dauki Bitrus, da Yakubu, da Yahaya. Ya fara jin wahala mutuka tare da damuwa kwarai.
34 And saith to them, My soul is exceeding sorrowful to death: tarry ye here, and watch.
Sai ya ce masu “Raina na shan wahala harma kamar in mutu. Ku dakata a nan, ku zauna a fadake”.
35 And he went forward a little, and fell on the ground, and prayed that, If it were possible, the hour might pass from him.
Da Yesu yayi gaba kadan, sai ya fadi kasa yayi addu'a yana cewa idan mai yiwuwa ne “A dauke masa wannan sa'a daga gare shi.
36 And he said, Abba, Father, all things [are] possible to thee; take away this cup from me: nevertheless, not what I will, but what thou wilt.
Ya ce “Ya Abba Uba, kome mai yuwane gare ka, ka dauke mini kokon wahalan nan, duk da haka ba nufina ba sai dai naka”.
37 And he cometh, and findeth them sleeping, and saith to Peter, Simon, sleepest thou? couldst not thou watch one hour?
Da komowarsa ya same su suna barci, sai ya ce wa Bitrus, Siman barci kake? Ashe, ba za ka iya zama a fadake ko da sa'a daya ba?
38 Watch ye and pray, lest ye enter into temptation. The spirit truly [is] ready, but the flesh [is] weak.
Ku zauna a fadake, kuyi addu'a kada ku fada cikin jaraba. Lalle ruhu na da niyya amma jiki raunana ne.
39 And again he went away, and prayed, and spoke the same words.
Sai ya sake komawa, yayi addu'a, yana maimaita kalmominsa na farko.
40 And when he returned, he found them asleep again (for their eyes were heavy: ) neither knew they what to answer him.
Har wa yau kuma ya sake dawowa, ya same su suna barci don barci ya cika masu idanu kwarai, sun kuwa kasa ce masa kome.
41 And he cometh the third time, and saith to them, Sleep on now, and take [your] rest: it is enough, the hour is come; behold, the Son of man is betrayed into the hands of sinners.
Ya sake komowa karo na uku yace masu “har yanzu barci kuke yi kuna hutawa? Ya isa haka! Lokaci yayi, an bada Dan Mutum ga masu zunubi”.
42 Rise, let us go; lo, he that betrayeth me is at hand.
Ku tashi mutafi kun ga, ga mai bashe ni nan ya kusato.”
43 And immediately while he was yet speaking, cometh Judas, one of the twelve, and with him a great multitude with swords and staffs, from the chief priests, and the scribes, and the elders.
Nan da nan, kafin ya rufe baki sai ga Yahuza, daya daga cikin sha biyun da taron jama'a rike da takkuba da kulake. Manyan firistoci da malaman attaura da shugabanni suka turo su.
44 And he that betrayed him, had given them a token, saying, Whomsoever I shall kiss, that same is he; take him, and lead [him] away safely.
Mai bashe shi din nan ya riga ya kulla da su cewa “Wanda zan yi wa sumba shine mutumin, ku kama shi ku tafi da shi a tsare.
45 And as soon as he was come, he goeth immediately to him, and saith, Master, master; and kissed him.
Da isowarsa kuwa, sai ya zo wurin Yesu ya ce “Ya malam!”. Sai ya sumbace shi.
46 And they laid their hands on him, and took him.
Su kuwa suka kama shi, suka tafi da shi.
47 And one of them that stood by drew a sword, and smote a servant of the high priest, and cut off his ear.
Amma daya daga cikin na tsaye ya zaro takobinsa ya kai wa bawan babban firist sara, ya yanke masa kunne.
48 And Jesus answered and said to them, Have ye come out, as against a thief, with swords and [with] staffs to take me?
Sai Yesu ya ce “kun fito kamar masu kama yan fashi da takkuba da kulake, domin ku kama ni?
49 I was daily with you in the temple, teaching, and ye took me not: but the scriptures must be fulfilled.
Lokacin da nake koyarwa a Haikali, kowace rana da ku, baku kama ni ba. Amma anyi haka ne domin a cika abinda Nassi ya fada.”
50 And they all forsook him, and fled.
Daga nan duk wadanda suke tare da Yesu suka yashe shi, suka tsere.
51 And there followed him a certain young man, having a linen cloth cast about [his] naked [body]; and the young men laid hold on him.
Wani saurayi, daga shi sai mayafi ya bi shi, suka kai masa cafka.
52 And he left the linen cloth, and fled from them naked.
Shi kuwa ya bar masu mayafin ya gudu tsirara.
53 And they led Jesus away to the high priest: and with him were assembled all the chief priests, and the elders and the scribes.
Daga nan suka tafi da Yesu wurin babban firist. a can suka tara dattawa duk da manyan firistoci da shugabanni da marubuta, suka taru a wurinsa.
54 And Peter followed him at a distance, even into the palace of the high priest: and he sat with the servants, and warmed himself at the fire.
Bitrus kuwa ya bi shi daga nesa har cikin gidan babban firist. Ya zauna tare da dogaran Haikalin, yana jin dumin wuta.
55 And the chief priests, and all the council sought for testimony against Jesus to put him to death; and found none.
Sai, manyan firistoci da duk 'yan majalisa Yahudawa suka nemi shaidar da za a tabbatar a kan Yesu, don su samu su kashe shi. Amma basu samu ba.
56 For many bore false testimony against him, but their testimony agreed not together.
Da yawa kuma suka yi masa shaidar Zur (Karya), amma bakin su bai zama daya ba.
57 And there arose certain, and bore false testimony against him, saying,
Sai wadansu kuma suka taso suka yi masa shaidar zur (karya) suka ce.
58 We heard him say, I will destroy this temple that is made with hands, and within three days I will build another made without hands.
“Mun ji ya ce, wai zai rushe haikalin nan da mutane suka gina, ya sake gina wani cikin kwana uku, ba kuwa ginin mutum ba”.
59 But neither so did their testimony agree together.
Duk da haka, sai shaidar tasu bata zo daya ba.
60 And the high priest stood up in the midst, and asked Jesus, saying, Answerest thou nothing? what is it which these testify against thee?
Sai babban firist ya mike a tsakanin su, ya tambayi Yesu yace “Ba ka da wata amsa game da shaidar da mutanen nan suke yi a kanka?
61 But he held his peace, and answered nothing. Again the high priest asked him, and said to him, Art thou the Christ, the Son of the Blessed?
Amma yayi shiru abinsa, bai ce kome ba. Sai babban firist din ya sake tambayarsa “To, ashe kai ne Allmasihu Dan Madaukaki?
62 And Jesus said, I am: and ye shall see the Son of man sitting on the right hand of power, and coming in the clouds of heaven.
Yesu ya ce “Nine. Za ku kuwa ga Dan Mutum zaune dama ga mai iko, yana kuma zuwa cikin gajimare”.
63 Then the high priest rent his clothes, and saith, What need we any further witnesses?
Sai babban firist ya kyakketa tufafinsa yace “Wacce shaida kuma zamu nema?
64 Ye have heard the blasphemy: what think ye? And they all condemned him to be guilty of death.
Kun dai ji sabon da yayi! Me kuka gani? Duk suka yanke masa hukunci akan ya cancanci kisa.
65 And some began to spit on him, and to cover his face, and to buffet him, and to say to him, Prophesy: and the servants struck him with the palms of their hands.
Wadansu ma suka fara tottofa masa yau, suka daure masa idanu, suka bubbuge shi suna cewa “Yi annabci” Dogaran kuma suka yi ta marinsa.
66 And as Peter was below in the palace, there cometh one of the maids of the high priest:
Bitrus kuwa na kasa a filin gida, sai wata baranyar babban firist ta zo.
67 And when she saw Peter warming himself, she looked upon him, and said, And thou also wast with Jesus of Nazareth.
Da ta ga Bitrus na jin dumi, ta yi masa kallon gaske ta ce “Kaima ai tare kake da banazaren nan Yesu”.
68 But he denied, saying, I know not, neither do I understand what thou sayest. And he went out into the porch; and the cock crowed.
Amma ya musa ya ce “Ni ban ma san abinda kike fada ba balle in fahimta”. Sai ya fito zaure. Sai zakara yayi cara.
69 And a maid saw him again, and began to say to them that stood by, This is [one] of them.
Sai baranyar ta ganshi, ta sake ce wa wadanda ke tsaitsaye a wurin, “Wannan ma daya daga cikinsu ne”.
70 And he denied it again. And a little after, they that stood by said again to Peter, Surely thou art [one] of them: for thou art a Galilean, and thy speech agreeth [thereto].
Amma ya sake musawa, jim kadan sai na tsaitsayen suka ce wa Bitrus “Lalle kai ma dayansu ne don ba Galile ne kai”.
71 But he began to curse and to swear, [saying], I know not this man of whom ye speak.
Sai ya fara la'anta kansa yana ta rantsuwa yana ce wa “Ban ma san mutumin nan da kuke fada ba”.
72 And the second time the cock crowed. And Peter called to mind the word that Jesus said to him, Before the cock shall crow twice, thou wilt deny me thrice. And when he thought thereon, he wept.
Nan da nan sai zakara ya yi cara ta biyu, Bitrus kuwa ya tuna da maganar Yesu a gare shi cewa “Kafin zakara ya yi cara ta biyu, za ka yi musun sani na sau uku”. Da ya tuno haka, sai ya fashe da kuka.

< Mark 14 >