< Luke 9 >
1 Then he called his twelve disciples together, and gave them power and authority over all demons, and to cure diseases.
Ya kira almajiransa goma sha biyu, ya ba su iko su fitar da kowanne irin aljani, su kuma warkar da cututtuka daga mutane.
2 And he sent them to preach the kingdom of God, and to heal the sick.
Ya aike su, su yi wa'azin mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya.
3 And he said to them, Take nothing for [your] journey, neither staffs, nor bag, neither bread, neither money; neither have two coats apiece.
Ya ce masu, “Kada ku dauki komi tare da ku domin wannan tafiya. Kada ku dauki sanda, ko jakar matafiyi, ko gurasa, ko kudi - Kada ma ku dauki taguwa biyu.
4 And into whatever house ye enter, there abide, and thence depart.
Dukan gidan da ku ka shiga, ku zauna a gidan har zuwa lokacin da za ku tafi daga wannan yankin.
5 And whoever will not receive you, when ye go out of that city, shake off the very dust from your feet for a testimony against them.
Dukan wadanda ba su marabce ku ba, sa'adda ku ke barin wannan gari, ku karkabe kurar kafufunku a matsayin shaida a kansu.”
6 And they departed, and went through the towns, preaching the gospel, and healing every where.
Daga nan sai almajiran suka tafi zuwa cikin kauyuka, suka yi ta shelar bishara, su na warkar da mutane a ko'ina.
7 Now Herod the tetrarch heard of all that was done by him: and he was perplexed, because that it was said by some, that John had risen from the dead;
Ana nan Hirudus, mai mulki, ya ji labarin dukan abubuwan da su ke faruwa. Ya yi mamaki saboda wadansu mutane suna cewa Yahaya mai yin Baftisma ne ya sake dawowa da ransa.
8 And by some, that Elijah had appeared; and by others, that one of the ancient prophets had risen again.
Wadansu kuma suna cewa, annabi Iliya ne ya sake bayyana, wadansu kuma suna cewa daya daga cikin annabawa na da can ne ya sake bayyana da rai.
9 And Herod said, John have I beheaded; but who is this of whom I hear such things? And he desired to see him.
Hirudus ya ce, “Ba zai yiwu Yahaya ne ba, domin na datse masa kai. To, wanene wannan da ni ke jin wadannan abubuwa a kansa?” Daga nan sai ya cigaba da neman hanyar da zai ga Yesu.
10 And the apostles, when they had returned, told him all that they had done. And he took them, and went aside privately into a desert place, belonging to the city called Bethsaida.
Sa'adda manzannin suka dawo daga tafiyarsu, suka gaya wa Yesu dukan abubuwan da suka yi. Daga nan sai ya dauke su domin su tafi tare da shi zuwa garin Baitsaida.
11 And the people, when they knew [it], followed him: and he received them, and spoke to them of the kingdom of God, and healed them that had need of healing.
Amma sa'adda taron suka ji inda Yesu ya tafi, sai suka bi shi can. Ya marabce su ya yi masu jawabi a kan mulkin Allah, kuma ya warkar da wadanda su ke bukatar warkarwa.
12 And when the day began to decline, then came the twelve, and said to him, Send the multitude away, that they may go into the towns and country around, and lodge, and get victuals: for we are here in a desert place.
Da yake yamma ta fara yi, sai almajiransa goma sha biyu suka zo suka ce da shi, “Idan ka yarda ka sallami wannan babban taron mutane dominsu shiga cikin kauyuka, da ke kewaye da gonaki, dominsu sami abinci da wuraren da za su kwana, da yake mu na nan a wurin da ba kowa.”
13 But he said to them, Give ye them to eat. And they said, We have no more than five loaves and two fishes; except we should go and buy provisions for all this people.
Amma sai ya ce da su, “Ku ba su abin da za su ci.” Suka amsa masa, “Dukan abin da muke da shi shine, 'Yan dunkulen gurasa biyar da 'yan kifaye guda biyu, ba za mu iya zuwa mu sawo abincin da zai ishi mutanen nan su duka ba.”
14 For they were about five thousand men. And he said to his disciples, Make them sit down by fifties in a company.
Mutanen da suke wurin sun kai kimanin mazaje dubu biyar. Sai Yesu ya ce da almajiran, “Ku ce da mutanen su zauna kungiya-kungiya, mutane hamsin a kowacce kungiya.”
15 And they did so, and made them all sit down.
Sai almajiran suka yi haka, dukan mutanen suka zauna.
16 Then he took the five loaves, and the two fishes, and looking up to heaven, he blessed them, and broke, and gave to the disciples to set before the multitude.
Ya dauki dunkulen gurasan guda biyar, da kifin guda biyu, yana dubawa zuwa sama ya albakarce su, sa'annan ya gutsuttsura, ya ba almajiran domin su rarraba wa mutane.
17 And they ate, and were all satisfied: and there was taken up of fragments that remained to them, twelve baskets.
Dukansu suka ci kowa ya koshi. Daga nan almajiran suka tattara sauran abin da ya rage, har kwanduna goma sha biyu suka cika!
18 And it came to pass, as he was in retirement praying, his disciples were with him; and he asked them, saying, Who say the people that I am?
Wata rana Yesu yana yin addu'a shi kadai, sai almajiransa suka zo sai ya tambaye su, “Wa mutane suke cewa da ni?”
19 They answering, said, John the Baptist; but some [say], Elijah; and others [say], that one of the ancient prophets is risen again.
Suka amsa, “Wadansu suna cewa, Yahaya mai yin Baftisma, wadansu suna cewa kai annabi Iliya ne, har yanzu wadansu suna cewa kai wani cikin annabawa na da can ne ya dawo da rai.”
20 He said to them, But who say ye that I am? Peter answering, said, Christ of God.
Ya tambaye su, “Ku fa? Wa kuke cewa da ni?” Bitrus ya amsa, “Kai Almasihu ne wanda ya zo daga wurin Allah.”
21 And he strictly charged them, and commanded [them] to tell no man that thing,
Sai Yesu ya gargade su da karfi, kada su gayawa kowa haka tukuna.
22 Saying, The Son of man must suffer many things, and be rejected by the elders, and chief priests, and scribes, and be put to death, and be raised the third day.
Sa'annan ya ce, “Dan Mutum dole ya sha wahalar abubuwa da yawa; dattawa za su ki shi da manyan fristoci da marubuta, sa'annan za a kashe shi. Bayan kwana uku, za a tashe shi da rai.”
23 And he said to [them] all, If any [man] will come after me, let him deny himself, and take up his cross daily, and follow me.
Sai ya ce da su duka, “Dukan wanda ya ke so ya biyo ni, dole ne ya yi musun kansa, ya dauki gicciyen sa kulluyomin, ya biyo ni.
24 For whoever will save his life, shall lose it: but whoever will lose his life for my sake, the same shall save it.
Dukan wanda yake so ya ceci ransa, za ya rasa shi, amma dukan wanda ya ba da ransa domina, za ya cece shi.
25 For what is a man profited, if he shall gain the whole world, and lose himself, or be cast away?
Wacce riba mutum zai samu idan ya sami duniya duka, amma ya rasa ransa?
26 For whoever shall be ashamed of me, and of my words, of him will the Son of man be ashamed, when he shall come in his own glory, and [in that of his] Father, and of the holy angels.
Dukan wanda yake jin kunya ta da magana ta, Dan Mutum ma zai ji kunyarsa, sa'adda ya dawo cikin darajarsa da darajar Uba da ta mala'iku masu tsarki.
27 But I tell you in truth, there are some standing here who shall not taste death till they see the kingdom of God.
Amma ina gaya maku wannan tabbas, wadansu cikinku da ke nan tsaye, ba za su mutu ba sai sun ga mulkin Allah.”
28 And it came to pass, about eight days after these sayings, he took Peter, and John, and James, and went up upon a mountain to pray.
Kwana takwas bayan Yesu ya fadi wadannan kalmomi, sai ya dauki Bitrus da Yahaya da Yakubu, ya hau kan dutse domin ya yi addu'a a can.
29 And as he prayed, the fashion of his countenance was altered, and his raiment [was] white [and] glistening.
Sa'anda ya ke yin addu'a sai yanayin fuskar sa ya canza sosai, tufafinsa kuma suka yi sheki da haske kamar walkiya.
30 And behold, there talked with him two men, who were Moses and Elijah.
Nan da nan sai ga mutane biyu suna magana da shi, wato Musa da Iliya.
31 Who appeared in glory, and spoke of his decease which he should accomplish at Jerusalem.
Suka bayyana da daraja kewaye da su, suka yi magana da Yesu a kan tafiyarsa wadda za ta zo ba da dadewa ba a cikin Urushalima.
32 But Peter and they that were with him were heavy with sleep: and when they were awake, they saw his glory, and the two men that stood with him.
Bitrus da almajiran da suke tare da shi barci mai nauyi ya dauke su. Sa'adda suka farka sai su suka ga daukakar Yesu; kuma suka ga mutanen su biyu da ke tsaye tare da shi.
33 And it came to pass, as they departed from him, Peter said to Jesus, Master, it is good for us to be here: and let us make three tabernacles; one for thee, and one for Moses, and one for Elijah: not knowing what he said.
Sa'adda Musa da Iliya suke shirin su bar wurin Yesu, sai Bitrus ya ce, “Ya shugaba, ya yi kyau da muke a nan. Zai yi kyau mu yi runfuna uku, daya dominka, daya domin Musa, daya kuma domin Iliya.” Amma hakika bai san abin da ya ke fadi ba.
34 While he was thus speaking, there came a cloud and overshadowed them: and they feared as they entered into the cloud.
Sa'adda yake fadin haka sai wani girgije ya zo ya rufe su. Sai suka ji tsoro sa'adda girgijen ya kewaye su.
35 And there came a voice out of the cloud, saying, This is my beloved Son: hear him.
Sai ga wata murya daga cikin girgijen tana cewa, “Wannan Dana ne wanda na zaba, ku ji shi.”
36 And when the voice was past, Jesus was found alone. And they kept [it] close, and told no man in those days any of those things which they had seen.
Sa'adda muryar ta gama magana, Yesu yana nan shi kadai. Suka yi shiru ba su iya cewa kome ba a kan abin da suka gani a kwanakin nan.
37 And it came to pass, that on the next day, when they had come down from the hill, many people met him.
Washe gari, da suka sauko daga kan dutsen, sai taron mutane da yawa suka zo wurinsa.
38 And behold, a man of the company cried out, saying, Master, I beseech thee look upon my son: for he is my only child.
Nan da nan, wani mutum daga cikin taron mutanen ya yi magana da karfi, “Mallam, kayi wani abu dominka taimaki da na, shi kadai ne gare ni.
39 And lo, a spirit taketh him, and he suddenly crieth out; and it teareth him that he foameth, and bruising him, hardly departeth from him.
Mugun ruhu ya kan hau kansa, ya sa shi ya yi ta magowa. Ya kan girjiza shi da karfi ya sa bakinsa ya yi ta kumfa. Da kyar ya ke rabuwa da shi, kuma ya kan ji masa ciwo ba kadan ba bayan da ya bar shi.
40 And I besought thy disciples to cast him out, and they could not.
Na roki almajiran ka su umurci mugun ruhun ya fita daga cikinsa, amma ba su iya ba!”
41 And Jesus answering, said, O faithless and perverse generation, how long shall I be with you, and suffer you? Bring thy son hither.
Yesu, ya amsa, ya ce, “Ku karkatattun tsara marasa bangaskiya, har yaushe zan zauna da ku ina jimrewa da ku? “Kawo yaronka anan.”
42 And as he was yet coming, the demon threw him down, and tore [him]. And Jesus rebuked the unclean spirit, and healed the child, and delivered him again to his father.
Sa'adda yaron yake zuwa, sai mugun ruhun ya fyada yaron a kasa, ya jijjiga shi sosai. Amma Yesu ya tsauta wa mugun ruhun, ya warkar da yaron. Sa'annan ya mika yaron wurin mahaifinsa.
43 And they were all amazed at the mighty power of God. But while they were all wondering at all things which Jesus did, he said to his disciples,
Dukansu suka yi mamaki da girman ikon Allah. Amma sa'anda suke ta yin mamaki a kan dukan al'ajiban da ya yi, ya ce da almajiransa,
44 Let these sayings sink down into your ears: for the Son of man will be delivered into the hands of men.
“Ku saurara da kyau a kan abin da zan gaya maku, ba da dadewa ba za a bada Dan Mutum ga mutane.”
45 But they understood not this saying, and it was hid from them, that they perceived it not: and they feared to ask him concerning that saying.
Amma almajiran ba su gane abin da yake nufi da haka ba, an hana su fahimta, domin kada su gane abin da ya ke nufi tukuna, kuma suna jin tsoron su tambaye shi.
46 Then there arose a reasoning among them, which of them should be greatest.
Wani lokaci, almajiran suka fara gardama a tsakaninsu game da wanene za ya zama mafi girma a cikinsu.
47 And Jesus perceiving the thought of their heart, took a child, and set him by him,
Amma Yesu ya san abin da suke tunani a zuciyarsu, sai ya kawo dan karamin yaro ya tsaya a kusa da shi,
48 And said to them, Whoever shall receive this child in my name, receiveth me; and whoever shall receive me, receiveth him that sent me: for he that is least among you all, the same shall be great.
sai ya ce da su, “Idan wani ya karbi dan karamin yaro kamar wannan saboda ni, dai dai yake da ya karbe ni. Idan kuma wani ya karbe ni, ya karbi wanda ya aiko ni kenan. Wanda yake mafi kankanta a cikinku, shi ne mafi mahimmanci.”
49 And John answered and said, Master, we saw one casting out demons in thy name; and we forbad him, because he followeth not with us.
Yahaya ya amsa yace, “Ya shugaba, mun ga wani mutum yana ba miyagun ruhohi umarni su fita daga cikin mutane da sunanka. Sai muka ce da shi ya dena yin haka saboda baya tare da mu.”
50 And Jesus said to him, Forbid [him] not: for he that is not against us, is for us.
Amma Yesu ya ce, “Kada ku hana shi yin haka, domin dukan wanda ba ya gaba da ku, yana tare da ku.”
51 And it came to pass, when the time was come that he should be received up, he steadfastly set his face to go to Jerusalem,
Sa'adda rana ta kusato da zai hawo zuwa sama, ya kudurta sosai zai tafi Urushalima.
52 And sent messengers before his face: and they went and entered into a village of the Samaritans, to make ready for him.
Ya aiki wadansu manzanni su shirya wuri dominsa kafin ya zo. Suka shiga wani kauye a cikin kauyen Samariya domin su shirya masa wuri a can.
53 And they did not receive him, because his face was as though he would go to Jerusalem.
Amma mutanen can ba su karbe shi ba tun da ya ke Urushalima zai tafi.
54 And when his disciples James and John saw [this], they said, Lord, wilt thou that we command fire to come down from heaven, and consume them, even as Elijah did?
Sa'adda biyu daga cikin almajiransa, wato Yakubu da Yahaya suka ga haka, suka ce, “Ubangiji, kana so mu umarci wuta ta sauko daga sama, ta hallaka su?”
55 But he turned, and rebuked them, and said, Ye know not what manner of spirit ye are of.
Amma, ya juya ya tsauta masu.
56 For the Son of man is not come to destroy men's lives, but to save [them]. And they went to another village.
Sai suka tafi wani kauye dabam.
57 And it came to pass, that as they were going in the way, a certain [man] said to him, Lord, I will follow thee whithersoever thou goest.
Da suna cikin tafiya a kan hanya, sai wani mutum ya ce da shi, “Zan bi ka dukan inda za ka tafi.”
58 And Jesus said to him, Foxes have holes, and birds of the air [have] nests; but the Son of man hath not where to lay [his] head.
Yesu ya amsa masa, “Dila suna da ramuka a kasa inda za su shiga, tsuntsaye kuma suna da sheka, amma Dan Mutum ba shi da inda zai kwanta.”
59 And he said to another, Follow me. But he said, Lord, suffer me first to go and bury my father.
Yesu, ya ce da wani mutumin kuma, “Ka biyo ni.” Amma mutumin ya ce, “Ubangiji, ka bari in koma gida in bizine mahaifina tukuna.”
60 Jesus said to him, Let the dead bury their dead: but go thou and preach the kingdom of God.
Amma Yesu ya ce masa, “Ka bar matattu su bizine matattunsu; amma kai ka tafi ka yi wa mutane shelar mulkin Allah a ko'ina.”
61 And another also said, Lord, I will follow thee; but let me first go [and] bid them farewell who are at my house.
Wani kuma ya ce, “Ubangiji zan tafi tare da kai, amma bari in je gida inyi ban kwana da mutanena tukuna.”
62 And Jesus said to him, No man having put his hand to the plow, and looking back, is fit for the kingdom of God.
Yesu ya ce da shi, “Dukan wanda ya fara huda a gonarsa idan ya dubi baya, bai isa ya shiga mulkin Allah ba.”