< Luke 18 >

1 And he spoke a parable to them [to this end], that men ought always [to] pray, and not to faint;
Ya kuma ba su wani misali cewa ya kamata kullum su yi addu'a kada kuma su karaya,
2 Saying, There was in a city a judge, who feared not God, neither regarded man.
yace, “A wani gari an yi wani alkali mara tsoron Allah, kuma baya ganin darajan mutane.
3 And there was a widow in that city; and she came to him, saying, Avenge me of my adversary.
Akwai wata mace gwauruwa a wannan garin, wadda ta rika zuwa wurinsa, tana ce masa, 'Ka taimake ni yanda zan sami adalci a kan abokin gaba na.'
4 And he would not for a while: but afterward he said within himself, Though I fear not God, nor regard man;
An dade bai so ya taimaka mata, amma daga baya sai ya ce a ransa, 'ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma darajanta mutane,
5 Yet because this widow troubleth me, I will avenge her, lest by her continual coming she weary me.
duk da haka saboda gwauruwar nan ta dame ni, zan taimake ta domin ta sami adalci, yadda ba za ta gajiyar da ni da zuwanta wurina ba.'”
6 And the Lord said, Hear what the unjust judge saith.
Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alkalin nan marar gaskiya ya fada.
7 And will not God avenge his own elect, who cry day and night to him, though he beareth long with them?
A yanzu Allah ba zai biya wa zababbunsa da suke yi masa kuka dare da rana hakkinsu ba? Zai yi jinkiri a wajen taimakonsu ne?
8 I tell you that he will avenge them speedily. Nevertheless, when the Son of man cometh, will he find faith on the earth?
Ina gaya maku, zai biya masu hakkin su da wuri. Amma sa'adda Dan Mutum ya zo, zai tarar da bangaskiya a duniya?”
9 And he spoke this parable to certain who trusted in themselves that they were righteous, and despised others:
Ya sake ba da misalin nan ga wadansu masu amincewa da kansu, wai su masu adalci ne, har suna raina sauran mutane,
10 Two men went up into the temple to pray; the one a Pharisee, and the other a publican.
“Wadansu mutane biyu suka shiga haikali domin yin addu'a - daya Bafarise, dayan kuma mai karbar haraji ne.
11 The Pharisee stood and prayed thus with himself, God, I thank thee, that I am not as other men [are], extortioners, unjust, adulterers, or even as this publican.
Sai Bafarisen ya mike, ya yi addu'a a kan wadannan abubuwa game da kansa, 'Allah, na gode maka, da cewa ni ba kamar sauran mutane dake mazambata ba, ko marasa adalci, ko mazinata, ko kamar wannan mai karbar harajin.
12 I fast twice in the week, I give tithes of all that I possess.
Duk mako ina azumi sau biyu. Nakan bayar da zakkar dukan abin da na samu.'
13 And the publican, standing afar off, would not lift up so much as [his] eyes to heaven, but smote upon his breast, saying, God be merciful to me a sinner.
Amma mai karbar harajin kuwa yana tsaye daga can nesa, bai yarda ya daga kai sama ba, sai dai yana bugun kirjin sa, yana cewa, 'Allah, ka yi mini jinkai, ni mai zunubi.'
14 I tell you, this man went down to his house justified [rather] than the other: for every one that exalteth himself shall be abased; and he that humbleth himself shall be exalted.
Ina gaya maku, wannan mutum ya koma gidansa baratacce, ba kamar dayan ba, domin dukan wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, amma duk wanda kaskantar da kansa kuwa daukaka shi za a yi.”
15 And they brought to him also infants, that he would touch them: but when [his] disciples saw [it], they rebuked them.
Sai mutanen suka kawo masa jariransu, domin ya taba su, da almajiransa suka ga haka, sai suka kwabe su.
16 But Jesus called them [to him], and said, Suffer little children to come to me, and forbid them not: for of such is the kingdom of God.
Amma Yesu ya kira su wurinsa, ya ce, “Ku bar yara kanana su zo wurina, kada ku hana su. Ai mulkin Allah na irin su ne.
17 Verily I say to you, Whoever shall not receive the kingdom of God as a little child, shall in no wise enter into it.
Gaskiya ina gaya maku, duk wanda bai karbi mulkin Allah kamar karamin yaro ba, lallai ba zai shige shi ba.”
18 And a certain ruler asked him, saying, Good Master, what shall I do to inherit eternal life? (aiōnios g166)
Wani shugaban jama'a ya tambaye shi ya ce “Malam managarci, me zan yi in gaji rai Madawwami?” (aiōnios g166)
19 And Jesus said to him, Why callest thou me good? none [is] good, save one, [that is] God.
Yesu ya ce masa, “Don me ka kira ni managarci? Babu wani managarci sai Allah kadai.
20 Thou knowest the commandments, Do not commit adultery, Do not kill, Do not steal, Do not bear false witness, Honor thy father and thy mother.
Ka dai san dokokin - kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar karya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.”
21 And he said, All these have I kept from my youth.
Sai shugaban ya ce, “Dukan wadannan abubuwa na kiyaye su tun a kuruciya ta.”
22 Now when Jesus heard these things, he said to him, Yet lackest thou one thing: sell all that thou hast, and distribute to the poor, and thou shalt have treasure in heaven: and come, follow me.
Da Yesu ya ji haka, ya ce masa, “Abu daya ne kadai ya rage maka. Dole ne ka sayar da dukan mallakarka, ka rarraba wa gajiyayyu, za ka kuma sami wadata a sama - sa'annan ka zo ka biyoni.”
23 And when he heard this, he was very sorrowful: for he was very rich.
Amma da mai arzikin ya ji wadannan abubuwa, sai yayi bakin ciki kwarai, don shi mai arziki ne sosai.
24 And when Jesus saw that he was very sorrowful, he said, How hardly will they that have riches enter into the kingdom of God!
Yesu kuwa, da ya ga ransa ya baci, sai ya ce, “Yana da wuya masu dukiya su shiga mulkin Allah!
25 For it is easier for a camel to go through a needle's eye, than for a rich man to enter into the kingdom of God.
Zai zama da sauki rakumi ya shiga kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
26 And they that heard [it], said, Who then can be saved?
Wadanda suka ji wannan magana suka ce, “Idan hakane wa zai sami ceto kenan?”
27 Then he said, The things which are impossible with men, are possible with God.
Yesu ya amsa, “Abin da ya fi karfin mutum, mai yiwuwa ne a gun Allah.”
28 Then Peter said, Lo, we have left all, and followed thee.
Sai Bitrus ya ce, “To, ga shi mun bar mallakarmu, mun bi ka.”
29 And he said to them, Verily I say to you, there is no man that hath left house, or parents, or brethren, or wife, or children for the sake of the kingdom of God,
Yesu ya ce masu, “Hakika, ina gaya maku, ba wanda zai bar gida, ko matarsa, ko 'yan'uwansa, ko iyayensa, ko kuma 'ya'yansa, saboda mulkin Allah,
30 Who shall not receive manifold more in this present time, and in the world to come life everlasting. (aiōn g165, aiōnios g166)
sa'annan ya kasa samun ninkin ba ninkin a duniyan nan, da rai na har abada a duniya mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Then he took the twelve, and said to them, Behold, we go up to Jerusalem, and all things that are written by the prophets concerning the Son of man shall be accomplished.
Bayan da ya tara su goma sha biyun nan, ya ce masu, “Ga shi, muna tafiya zuwa Urushalima, duk abubuwan da aka rubuta game da Dan Mutum ta hannun annabawa zasu tabbata.
32 For he will be delivered to the Gentiles, and will be mocked, and spitefully treated, and spitted on;
Gama za a bashe shi ga al'ummai, a yi masa ba'a, a wulakanta shi, a kuma tofa masa miyau.
33 And they will scourge [him], and put him to death: and the third day he will rise again.
Za su yi masa bulala, su kashe shi, a rana ta uku kuma zai tashi.”
34 And they understood none of these things: and this saying was hid from them, neither knew they the things which were spoken.
Amma ba su fahimci ko daya daga cikin wadannan abubuwa ba, domin zancen nan a boye yake daga garesu, ba su ma gane abin da aka fada ba.
35 And it came to pass, that as he had come nigh to Jericho, a certain blind man sat by the way side begging;
Da ya kusato Yariko, ga wani makaho zaune a gefen hanya, yana bara,
36 And hearing the multitude passing by, he asked what it meant.
da ya ji taro na wucewa, sai ya tambaya ko menene.
37 And they told him, that Jesus of Nazareth was passing by.
Suka ce masa Yesu Banazarat ne yake wucewa.
38 And he cried, saying, Jesus, [thou] son of David, have mercy on me.
Sai makahon ya ta da murya mai karfi, ya ce, “Yesu, Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
39 And they who went before rebuked him, that he should hold his peace: but he cried so much the more, [Thou] son of David, have mercy on me.
Sai wadanda suke gaba suka kwabe shi, suna gaya masa ya yi shiru. Amma ya kara daga murya kwarai da gaske, yana cewa, “Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
40 And Jesus stood and commanded him to be brought to him: and when he had come near, he asked him,
Sai Yesu ya tsaya, ya umarta a kawo shi wurinsa. Da makahon ya zo kusa, sai Yesu ya tambaye shi,
41 Saying, What wilt thou that I shall do to thee? And he said, Lord, that I may receive my sight.
“Me kake so in yi maka?” Ya ce, “Ubangiji, ina so in samu gani.”
42 And Jesus said to him, Receive thy sight: thy faith hath saved thee.
Yesu ya ce masa, “Karbi ganin gari, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
43 And immediately he received his sight, and followed him, glorifying God: and all the people, when they saw [it], gave praise to God.
Nan take ya samu gani, ya bi Yesu, yana daukaka Allah. Ganin haka, sai duk jama'a suka yabi Allah.

< Luke 18 >