< Luke 1 >
1 Forasmuch as many have taken in hand to set forth in order a declaration of those things which are most surely believed among us,
Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
2 Even as they delivered them to us, who from the beginning were eye-witnesses, and ministers of the word;
kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
3 It seemed good to me also, having had perfect understanding of all things from the very first, to write to thee in order, most excellent Theophilus,
Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
4 That thou mayest know the certainty of those things in which thou hast been instructed.
Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
5 There was in the days of Herod the king of Judea, a certain priest named Zacharias, of the course of Abia: and his wife [was] of the daughters of Aaron, and her name [was] Elisabeth.
A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
6 And they were both righteous before God, walking in all the commandments and ordinances of the Lord blameless.
Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
7 And they had no child, because Elisabeth was barren, and they both were far advanced in years.
Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
8 And it came to pass, that, while he executed the priests' office before God in the order of his course,
Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
9 According to the custom of the priests' office, his lot was to burn incense when he went into the temple of the Lord.
Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
10 And the whole multitude of the people were praying without, at the time of incense.
Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
11 And there appeared to him an angel of the Lord, standing on the right side of the altar of incense.
A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
12 And when Zacharias saw [him], he was troubled, and fear fell upon him.
Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
13 But the angel said to him, Fear not, Zacharias: for thy prayer is heard; and thy wife Elisabeth shall bear thee a son, and thou shalt call his name John.
Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
14 And thou shalt have joy and gladness, and many shall rejoice at his birth.
Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
15 For he shall be great in the sight of the Lord, and shall drink neither wine nor strong drink; and he shall be filled with the Holy Spirit, even from his mother's womb.
Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
16 And many of the children of Israel shall he turn to the Lord their God.
Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
17 And he shall go before him in the spirit and power of Elijah, to turn the hearts of the fathers to the children, and the disobedient to the wisdom of the just; to make ready a people prepared for the Lord.
Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
18 And Zacharias said to the angel, By what shall I know this? for I am an old man, and my wife far advanced in years.
Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
19 And the angel answering, said to him, I am Gabriel, who stand in the presence of God; and am sent to speak to thee, and to show thee these glad tidings.
Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
20 And behold, thou shalt be dumb, and not able to speak, until the day that these things shall be performed, because thou believest not my words which shall be fulfilled in their season.
Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
21 And the people waited for Zacharias, and marveled that he tarried so long in the temple.
Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
22 And when he came out, he could not speak to them: and they perceived that he had seen a vision in the temple; for he beckoned to them, and remained speechless.
Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
23 And it came to pass, that as soon as the days of his ministration were accomplished, he departed to his own house.
Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
24 And after those days his wife Elisabeth conceived, and secluded herself five months, saying,
Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
25 Thus hath the Lord dealt with me in the days in which he looked on [me], to take away my reproach among men.
“Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
26 And in the sixth month, the angel Gabriel was sent from God to a city of Galilee, named Nazareth,
A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
27 To a virgin espoused to a man whose name was Joseph, of the house of David; and the virgin's name [was] Mary.
zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
28 And the angel came to her, and said, Hail, [thou that art] highly favored, the Lord [is] with thee: blessed [art] thou among women.
Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
29 And when she saw [him], she was troubled at his saying, and cast in her mind what manner of salutation this should be.
Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
30 And the angel said to her, Fear not, Mary: for thou hast found favor with God.
Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
31 And behold, thou shalt conceive in thy womb, and bring forth a son, and shalt call his name JESUS.
Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
32 He will be great, and will be called the Son of the Highest; and the Lord God will give to him the throne of his father David.
Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
33 And he will reign over the house of Jacob for ever, and of his kingdom there will be no end. (aiōn )
Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn )
34 Then said Mary to the angel, How shall this be, seeing I know not a man?
Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
35 And the angel answered and said to her, The Holy Spirit will come upon thee, and the power of the Highest will overshadow thee: therefore also that holy thing which shall be born of thee shall be called the Son of God.
Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
36 And behold, thy cousin Elisabeth, she hath also conceived a son in her old age; and this is the sixth month with her who was called barren:
Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
37 For with God nothing will be impossible.
Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
38 And Mary said, Behold the handmaid of the Lord, be it to me according to thy word. And the angel departed from her.
Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
39 And Mary arose in those days, and went into the hill-country with haste, into a city of Judah,
Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
40 And entered into the house of Zacharias, and saluted Elisabeth.
Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
41 And it came to pass, that when Elisabeth heard the salutation of Mary, the babe leaped in her womb: and Elisabeth was filled with the Holy Spirit.
Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
42 And she spoke with a loud voice, and said, Blessed [art] thou among women, and blessed [is] the fruit of thy womb.
Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
43 And whence [is] this to me, that the mother of my Lord should come to me?
Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
44 For lo, as soon as the voice of thy salutation sounded in my ears, the babe leaped in my womb for joy.
Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
45 And blessed [is] she that believed that there will be a performance of those things which were told her from the Lord.
Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
46 And Mary said, My soul doth magnify the Lord,
Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
47 And my spirit hath rejoiced in God my Savior.
kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
48 For he hath regarded the low estate of his handmaiden: for behold, from henceforth all generations will call me blessed.
Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
49 For he that is mighty hath done to me great things, and holy [is] his name.
Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
50 And his mercy [is] on them that fear him, from generation to generation.
Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
51 He hath shown strength with his arm; he hath scattered the proud in the imagination of their hearts.
Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
52 He hath put down the mighty from [their] seats, and exalted them of low degree.
Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
53 He hath filled the hungry with good things, and the rich he hath sent away empty.
Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
54 He hath sustained his servant Israel, in remembrance of [his] mercy;
Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
55 As he spoke to our fathers, to Abraham, and to his seed for ever. (aiōn )
(kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn )
56 And Mary abode with her about three months, and returned to her own house.
Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
57 Now Elisabeth's full time came that she should be delivered; and she brought forth a son.
Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
58 And her neighbors and her cousins heard that the Lord had shown great mercy upon her; and they rejoiced with her.
Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
59 And it came to pass, that on the eighth day they came to circumcise the child; and they called him Zacharias, after the name of his father.
Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
60 And his mother answered and said, Not [so]; but he shall be called John.
amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
61 And they said to her, There is none of thy kindred that is called by this name.
Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
62 And they made signs to his father, how he would have him called.
Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
63 And he asked for a writing-table, and wrote, saying, His name is John. And they all wondered.
Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
64 And his mouth was opened immediately, and his tongue [loosed], and he spoke, and praised God.
Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
65 And fear came on all that dwelt around them; and all these sayings were noised abroad throughout all the hill-country of Judea.
Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
66 And all they that had heard [them], laid [them] up in their hearts, saying, What manner of child will this be! And the hand of the Lord was with him.
Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
67 And his father Zacharias was filled with the Holy Spirit, and prophesied, saying,
Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
68 Blessed [be] the Lord God of Israel; for he hath visited and redeemed his people.
“Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
69 And hath raised up a horn of salvation for us, in the house of his servant David:
Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
70 As he spoke by the mouth of his holy prophets, who have been since the world began: (aiōn )
kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn )
71 That we should be saved from our enemies, and from the hand of all that hate us;
Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
72 To perform the mercy [promised] to our fathers, and to remember his holy covenant:
Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 The oath which he swore to our father Abraham,
rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
74 That he would grant to us, that we being delivered out of the hand of our enemies, might serve him without fear,
Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
75 In holiness and righteousness before him, all the days of our life.
a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
76 And thou, child, shalt be called the prophet of the Highest, for thou shalt go before the face of the Lord to prepare his ways;
I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
77 To give knowledge of salvation to his people, by the remission of their sins,
domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
78 Through the tender mercy of our God; by which the day-spring from on high hath visited us,
Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
79 To give light to them that sit in darkness and [in] the shades of death, to guide our feet into the way of peace.
domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
80 And the child grew, and became strong in spirit, and was in the deserts till the day of his showing to Israel.
Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.