< John 2 >

1 And the third day there was a marriage in Cana of Galilee; and the mother of Jesus was there.
Bayan kwana uku, akwai aure a Kana ta Galili, mahaifiyar Yesu kuma tana wurin.
2 And both Jesus was called, and his disciples, to the marriage.
An gayyaci Yesu da almajiransa zuwa auren.
3 And when they wanted wine, the mother of Jesus saith to him, They have no wine.
Da ruwan inabin ya kare, maihafiyar Yasu tace masa, “basu da ruwan inabi.”
4 Jesus saith to her, Woman, what have I to do with thee? my hour is not yet come.
Yesu yace mata, “Mace, me yasa kika zo wurina? Lokaci na bai yi ba tukuna”.
5 His mother saith to the servants, Whatever he saith to you, do [it].
Maihafiyarsa tace wa ma'aikatan, “Ku yi duk abin da yace maku.”
6 And there were set there six waterpots of stone, after the manner of the purifying of the Jews, containing two or three firkins apiece.
To akwai randunan ruwa na dutse guda shidda a wurin wadanda Yahudawa ke amfani da su domin al'adansu na tsarkakewa, kowace zata iya daukar durom guda.
7 Jesus saith to them, Fill the waterpots with water. And they filled them to the brim.
Yesu yace masu, “Cika randunan da ruwa”. Sai suka cika randunan makil.
8 And he saith to them, Draw out now, and bear to the governor of the feast. And they bore [it].
Sai yace wa ma'aikatan, “Ku diba daga ciki ku kai wa shugaban biki.” Sai suka yi hakannan.
9 When the ruler of the feast had tasted the water that was made wine, and knew not whence it was; (but the servants who drew the water knew) the governor of the feast called the bridegroom,
Shugaban bikin ya dandana ruwan da ya zama ruwan inabin, amma bai san inda ya fito ba (amma ma'aikatan wadanda suka jawo ruwan sun sani). Sai ya kira ango
10 And saith to him, Every man at the beginning presenteth good wine; and when men have well drank, then that which is worse: [but] thou hast kept the good wine until now.
yace masa, “Kowane mutum yakan raba ruwan inabi mai kyau da farko, kafin mai arhar bayan an shanye mai kyaun. Amma kai ka ajiye mai kyaun sai yanzu.”
11 This beginning of miracles Jesus performed in Cana of Galilee, and manifested his glory; and his disciples believed on him.
Wannan alama ta farko ce da Yesu yayi a Kana ta Galili, ya kuma bayyana daukakarsa, almajiransa kuma suka gaskata da shi.
12 After this he went down to Capernaum, he, and his mother, and his brethren, and his disciples; and they continued there not many days.
Bayan wannan, Yesu, da mahaifiyarsa, da 'yan'uwansa da almajiransa suka tafi Kafarnahum, kuma suka zauna can wasu 'yan kwanaki.
13 And the Jews' passover was at hand, and Jesus went up to Jerusalem,
To idin ketarewa na Yahudawa ya kusato, Yesu kuwa ya wuce zuwa Urushalima.
14 And found in the temple those that sold oxen, and sheep, and doves, and the changers of money, sitting:
Ya iske wadanda suke sayar da shanu da tumaki da tantabaru, masu canjin kudi kuma na zaune a wurin.
15 And when he had made a scourge of small cords, he drove them all out of the temple, and the sheep, and the oxen; and poured out the changers' money, and overthrew the tables;
Sai yayi tsumingiya da igiyoyi ya kore su duka daga cikin haikalin, duk da tumakin da shanun. Sai ya watsar da sulallan masu canjin kudin ya birkitar da teburansu.
16 And said to them that sold doves, Take these things hence: make not my Father's house a house of merchandise.
Yace wa masu sayar da tantabaru, “Ku fitar da wadannan abubuwa daga nan. Ku daina maida gidan Ubana wurin kasuwanci.”
17 And his disciples remembered that it was written, The zeal of thy house hath eaten me up.
Almajiransa suka tuna a rubuce yake, “Himma domin gidanka za ta cinye ni.”
18 Then answered the Jews, and said to him, What sign showest thou to us, seeing that thou doest these things?
Sai shugabannin Yahudawa suka amsa suka ce masa, “Wace alama za ka nuna mana, da shike kana yin wadannan abubuwan?”
19 Jesus answered and said to them, Destroy this temple, and in three days I will raise it up.
Yesu ya amsa, “Ku rushe wannan haikali, kuma a cikin kwana uku zan gina shi.”
20 Then said the Jews, Forty and six years was this temple in building, and wilt thou rear it up in three days?
Sai shugabanin Yahudawa suka ce, “An dauki shekaru arba'in da shidda kamin a gama gina wannan haikalin, za ka dau kwanaki uku kadai wajen gina shi?”
21 But he spoke of the temple of his body.
Amma yana nufin haikali na jikinsa ne.
22 When therefore he had risen from the dead, his disciples remembered that he had said this to them: and they believed the scripture, and the word which Jesus had spoken.
Bayan da aka tashe shi daga matattu, sai almajiransa suka tuna ya fadi haka, suka kuma ba da gaskiya ga nassi da wannan kalami da Yesu ya fada.
23 Now when he was in Jerusalem at the passover, in the feast [day], many believed in his name, when they saw the miracles which he performed.
Kuma, da yana Urushalima a idin ketarewa, a lokacin idin, mutane da yawa suka gaskata ga sunansa, sa'adda suka ga alamun da ya yi.
24 But Jesus did not commit himself to them, because he knew all [men].
Amma Yesu bai yadda da su ba domin ya san su duka,
25 And needed not that any should testify concerning man: for he knew what was in man.
saboda baya bukatar wani ya shaida masa game da mutum, domin ya san abinda ke cikin sa.

< John 2 >