< Job 36 >
1 Elihu also proceeded, and said,
Elihu ya ci gaba,
2 Suffer me a little, and I will show thee that [I have] yet to speak on God's behalf.
“Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
3 I will bring my knowledge from afar, and will ascribe righteousness to my Maker.
Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
4 For truly my words [shall] not [be] false: he that is perfect in knowledge [is] with thee.
Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
5 Behold, God [is] mighty, and despiseth not [any]: [he is] mighty in strength [and] wisdom.
“Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
6 He preserveth not the life of the wicked: but giveth right to the poor.
Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
7 He withdraweth not his eyes from the righteous: but with kings [are they] on the throne; yes, he doth establish them for ever, and they are exalted.
Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
8 And if [they are] bound in fetters, [and] are held in cords of affliction;
Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
9 Then he showeth them their work, and their transgressions that they have exceeded.
yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
10 He openeth also their ear to discipline, and commandeth that they return from iniquity.
Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
11 If they obey and serve [him], they shall spend their days in prosperity, and their years in pleasures.
In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
12 But if they obey not, they shall perish by the sword, and they shall die without knowledge.
Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
13 But the hypocrites in heart heap up wrath: they cry not when he bindeth them.
“Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
14 They die in youth, and their life [is] among the unclean.
Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
15 He delivereth the poor in his affliction, and openeth their ears in oppression.
Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
16 Even so would he have removed thee out of the strait [into] a broad place, where [there is] no straitness; and that which should be set on thy table [would be] full of fatness.
“Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
17 But thou hast fulfilled the judgment of the wicked: judgment and justice take hold [on thee].
Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
18 Because [there is] wrath, [beware] lest he take thee away with [his] stroke: then a great ransom cannot deliver thee.
Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
19 Will he esteem thy riches? [no], not gold, nor all the forces of strength.
Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
20 Desire not the night, when people are cut off in their place.
Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
21 Take heed, regard not iniquity: for this hast thou chosen rather than affliction.
Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
22 Behold, God exalteth by his power: who teacheth like him?
“An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
23 Who hath enjoined him his way? or who can say, Thou hast wrought iniquity?
Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
24 Remember that thou magnify his work, which men behold.
Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
25 Every man may see it; man may behold [it] afar off.
Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
26 Behold, God [is] great, and we know [him] not, neither can the number of his years be searched out.
Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
27 For he maketh small the drops of water: they pour down rain according to the vapor of it.
“Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
28 Which the clouds do drop [and] distill upon man abundantly.
Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
29 Also can [any] understand the spreadings of the clouds, [or] the noise of his tabernacle?
Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
30 Behold, he spreadeth his light upon it, and covereth the bottom of the sea.
Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
31 For by them he judgeth the people; he giveth food in abundance.
Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
32 With clouds he covereth the light; and commandeth it [not to shine] by [the] intervening [cloud].
Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
33 The noise of it showeth concerning it, the cattle also concerning the vapor.
Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.