< Job 32 >
1 So these three men ceased to answer Job, because he [was] righteous in his own eyes.
Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
2 Then was kindled the wrath of Elihu the son of Barachel the Buzite, of the kindred of Ram: against Job was his wrath kindled, because he justified himself rather than God.
Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
3 Also against his three friends was his wrath kindled, because they had found no answer, and [yet] had condemned Job.
Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
4 Now Elihu had waited till Job had spoken because they [were] older than he.
Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
5 When Elihu saw that [there was] no answer in the mouth of [these] three men, then his wrath was kindled.
Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
6 And Elihu the son of Barachel the Buzite answered and said, I [am] young, and ye [are] very old; wherefore I was afraid, and durst not show you my opinion.
Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
7 I said, Days should speak, and multitude of years should teach wisdom.
Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
8 But [there is] a spirit in man: and the inspiration of the Almighty giveth them understanding.
Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
9 Great men are not [always] wise: neither do the aged understand judgment.
Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
10 Therefore I said, Hearken to me; I also will show my opinion.
“Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
11 Behold, I waited for your words; I gave ear to your reasons, whilst ye searched out what to say.
Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
12 Yes, I attended to you, and behold, [there was] none of you that convinced Job, [or] that answered his words:
na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
13 Lest ye should say, We have found out wisdom: God thrusteth him down, not man.
Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
14 Now he hath not directed [his] words against me: neither will I answer him with your speeches.
Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
15 They were amazed, they answered no more: they left off speaking.
“Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
16 When I had waited, (for they spoke not, but stood still, [and] answered no more; )
Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
17 [I said], I will answer also my part, I also will show my opinion.
Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
18 For I am full of matter, the spirit within me constraineth me.
Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
19 Behold, my belly [is] as wine [which] hath no vent; it is ready to burst like new bottles.
a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
20 I will speak, that I may be refreshed: I will open my lips and answer.
Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
21 Let me not, I pray you, accept any man's person, neither let me give flattering titles to man.
Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
22 For I know not to give flattering titles; [in so doing], my Maker would soon take me away.
gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.