< Job 16 >
1 Then Job answered and said,
Sai Ayuba ya amsa,
2 I have heard many such things: miserable comforters [are] ye all.
“Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
3 Shall vain words have an end? or what emboldeneth thee that thou answerest?
Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
4 I also could speak as ye [do]: if your soul were in my soul's stead, I could heap up words against you, and shake my head at you.
Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
5 [But] I would strengthen you with my mouth and the moving of my lips should assuage [your grief].
Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
6 Though I speak, my grief is not assuaged: and [though] I forbear, what am I eased?
“Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
7 But now he hath made me weary: thou hast made desolate all my company.
Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
8 And thou hast filled me with wrinkles, [which] is a witness [against me]: and my leanness rising up in me beareth witness to my face.
Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
9 He teareth [me] in his wrath, who hateth me: he gnasheth upon me with his teeth; my enemy sharpeneth his eyes upon me.
Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
10 They have gaped upon me with their mouth; they have smitten me upon the cheek reproachfully; they have gathered themselves against me.
Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
11 God hath delivered me to the ungodly, and turned me over into the hands of the wicked.
Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
12 I was at ease, but he hath broken me asunder: he hath also taken [me] by my neck, and shaken me to pieces, and set me up for his mark.
Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
13 His archers encompass me; he cleaveth my reins asunder, and doth not spare; he poureth out my gall upon the ground.
maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
14 He breaketh me with breach upon breach, he runneth upon me like a giant.
Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
15 I have sewed sackcloth upon my skin, and defiled my horn in the dust.
“Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
16 My face is foul with weeping, and on my eyelids [are] the shades of death;
Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
17 Not for [any] injustice in my hands: also my prayer [is] pure.
duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
18 O earth, cover not thou my blood, and let my cry have no place.
“Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
19 Also now, behold, my witness [is] in heaven, and my record [is] on high.
Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
20 My friends scorn me: [but] my eye poureth out [tears] to God.
Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
21 O that one might plead for a man with God, as a man [pleadeth] for his neighbor!
a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
22 When a few years are come, then I shall go the way [whence] I shall not return.
“Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.