< Job 13 >
1 Lo, my eye hath seen all [this], my ear hath heard and understood it.
“Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
2 What ye know, [the same] do I know also: I [am] not inferior to you.
Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
3 Surely I would speak to the Almighty, and I desire to reason with God.
Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
4 But ye [are] forgers of lies, ye [are] all physicians of no value.
Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
5 O that ye would altogether hold your peace and it would be your wisdom.
In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
6 Hear now my reasoning, and hearken to the pleadings of my lips.
Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
7 Will ye speak wickedly for God? and talk deceitfully for him?
Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
8 Will ye accept his person? will ye contend for God?
Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
9 Is it good that he should search you out? or as one man mocketh another, do ye [so] mock him?
In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
10 He will surely reprove you, if ye do secretly accept persons.
Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
11 Shall not his excellence make you afraid? and his dread fall upon you?
Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
12 Your remembrances [are] like to ashes, your bodies to bodies of clay.
Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
13 Hold your peace, let me alone, that I may speak, and let come on me what [will].
“Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
14 Why do I take my flesh in my teeth, and put my life in my hand?
Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
15 Though he shall slay me, yet will I trust in him: but I will maintain my own ways before him.
Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
16 He also [shall be] my salvation: for a hypocrite shall not come before him.
lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
17 Hear diligently my speech, and my declaration with your ears.
Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
18 Behold now, I have ordered [my] cause; I know that I shall be justified.
Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
19 Who [is] he [that] will plead with me? for now, if I hold my tongue, I shall expire.
Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
20 Only do not two [things] to me: then will I not hide myself from thee.
“Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
21 Withdraw thy hand far from me: and let not thy dread make me afraid.
Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
22 Then call thou, and I will answer: or let me speak, and answer thou me.
Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
23 How many [are] my iniquities and sins? make me to know my transgression and my sin.
Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
24 Why hidest thou thy face, and holdest me for thy enemy?
Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
25 Wilt thou break a leaf driven to and fro? and wilt thou pursue the dry stubble?
Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
26 For thou writest bitter things against me, and makest me to possess the iniquities of my youth.
Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
27 Thou puttest my feet also in the stocks, and lookest narrowly to all my paths; thou settest a print upon the heels of my feet.
Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
28 And he, as a rotten thing, consumeth, as a garment that is moth-eaten.
“Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.